< Psaumes 116 >

1 J'aime l'Éternel, car il a entendu ma voix et mes supplications;
Ina ƙaunar Ubangiji, gama ya ji muryata; ya ji kukata ta neman jinƙai.
2 Car il a incliné son oreille vers moi; aussi je l'invoquerai toute ma vie.
Domin ya juye kunnensa gare ni, zan kira gare shi muddin ina da rai.
3 Les liens de la mort m'avaient entouré, les angoisses du Sépulcre m'avaient saisi; j'avais trouvé la détresse et la douleur. (Sheol h7585)
Igiyoyin mutuwa sun shaƙe ni, wahalar kabari sun zo a kaina; na cika da wahala da ɓacin rai. (Sheol h7585)
4 Mais j'invoquai le nom de l'Éternel: O Éternel, délivre mon âme!
Sai na kira ga sunan Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!”
5 L'Éternel est compatissant et juste, et notre Dieu fait miséricorde.
Ubangiji mai alheri ne da kuma mai adalci; Allahnmu yana cike da tausayi.
6 L'Éternel garde les petits; j'étais misérable, et il m'a sauvé.
Ubangiji yana tsare masu tawali’u; sa’ad da nake cikin tsananin bukata, ya cece ni.
7 Mon âme, retourne à ton repos, car l'Éternel t'a fait du bien.
Ka kwantar da hankali, ya raina, gama Ubangiji mai alheri ne a gare ka.
8 Car tu as délivré mon âme de la mort, mes yeux de pleurs, et mes pieds de chute.
Gama kai, ya Ubangiji, ka ceci raina daga mutuwa, idanuna daga hawaye, ƙafafuna daga tuntuɓe,
9 Je marcherai devant la face de l'Éternel sur la terre des vivants.
don in iya tafiya a gaban Ubangiji a ƙasar masu rai.
10 J'ai cru, c'est pourquoi j'ai parlé. J'ai été fort affligé.
Na gaskata, saboda haka na ce, “An azabtar da ni ƙwarai.”
11 Je disais dans mon agitation: Tout homme est menteur.
Kuma cikin rikicewana na ce, “Dukan mutane maƙaryata ne.”
12 Que rendrai-je à l'Éternel? Tous ses bienfaits sont sur moi.
Yaya zan sāka wa Ubangiji saboda dukan alherinsa gare ni?
13 Je prendrai la coupe des délivrances, et j'invoquerai le nom de l'Éternel.
Zan daga kwaf na ceto in kuma kira ga sunan Ubangiji.
14 Je rendrai mes vœux à l'Éternel, en présence de tout son peuple.
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa.
15 La mort des bien-aimés de l'Éternel est précieuse à ses yeux.
Abu mai daraja a gaban Ubangiji shi ne mutuwar tsarkakansa.
16 Je te prie, ô Éternel! car je suis ton serviteur, ton serviteur, fils de ta servante. Tu as délié mes liens.
Ya Ubangiji, da gaske ni bawanka ne; ni bawanka ne, ɗan baiwarka; ka’yantar da ni daga sarƙoƙi.
17 Je t'offrirai le sacrifice d'actions de grâces, et j'invoquerai le nom de l'Éternel.
Zan yi hadayar godiya gare ka in kuma kira bisa sunan Ubangiji.
18 Je rendrai mes vœux à l'Éternel, en présence de tout son peuple,
Zan cika alkawurana ga Ubangiji a gaban dukan mutanensa,
19 Dans les parvis de la maison de l'Éternel, au milieu de toi, Jérusalem. Louez l'Éternel!
a filayen gidan Ubangiji, a tsakiyarki, ya Urushalima. Yabi Ubangiji.

< Psaumes 116 >