< Psaumes 107 >

1 Célébrez l'Éternel, car il est bon, car sa miséricorde demeure à toujours!
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qu'ainsi disent les rachetés de l'Éternel, ceux qu'il a rachetés de la main de l'oppresseur,
Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
3 Et qu'il a rassemblés des pays d'orient et d'occident, de l'aquilon et du midi.
su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
4 Ils erraient par le désert, dans un chemin solitaire; ils ne trouvaient point de ville habitable.
Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
5 Ils étaient affamés et altérés; leur âme défaillait en eux.
Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
6 Alors ils ont crié à l'Éternel dans leur détresse; et il les a délivrés de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
7 Il les a conduits par le droit chemin, pour arriver à une ville habitable.
Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
8 Qu'ils célèbrent l'Éternel pour sa bonté, pour ses merveilles envers les fils des hommes!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
9 Car il a rassasié l'âme altérée, et rempli de biens l'âme affamée.
gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
10 Ceux qui habitaient les ténèbres et l'ombre de la mort, retenus dans l'affliction et dans les fers,
Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
11 Pour avoir été rebelles aux paroles de Dieu, et avoir méprisé le conseil du Très-Haut;
gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
12 Il avait humilié leur cœur par la souffrance; ils succombaient loin de tout secours.
Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
13 Alors ils ont crié à l'Éternel dans leur détresse; et il les a délivrés de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
14 Il les a tirés des ténèbres et de l'ombre de la mort; il a rompu leurs liens.
Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
15 Qu'ils célèbrent l'Éternel pour sa bonté, pour ses merveilles envers les fils des hommes!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
16 Car il a brisé les portes d'airain, et rompu les barreaux de fer.
gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Les insensés qui étaient affligés à cause de la voie de leurs trangressions et de leurs iniquités;
Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
18 Leur âme avait en horreur toute nourriture; ils touchaient aux portes de la mort.
Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
19 Alors ils ont crié à l'Éternel dans leur détresse; et il les a délivrés de leurs angoisses.
Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
20 Il a envoyé sa parole, et il les a guéris, et les a retirés de leurs tombeaux.
Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
21 Qu'ils célèbrent l'Éternel pour sa bonté, pour ses merveilles envers les fils des hommes!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
22 Qu'ils offrent des sacrifices d'actions de grâces, et racontent ses œuvres en chantant de joie!
Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
23 Ceux qui descendent sur la mer dans des navires, et qui trafiquent sur les grandes eaux,
Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
24 Ceux-là ont vu les œuvres de l'Éternel, et ses merveilles dans les lieux profonds.
Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
25 Il parla, et fit lever un vent de tempête, qui souleva les vagues de la mer.
Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
26 Ils montent aux cieux; ils descendent aux abîmes; leur âme se fond d'angoisse.
Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
27 Ils tournoient et chancellent comme un homme ivre; toute leur sagesse leur manque.
Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
28 Alors ils ont crié à l'Éternel dans leur détresse, et il les a retirés de leurs angoisses.
Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
29 Il arrête la tempête, la changeant en calme, et les ondes se taisent.
Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
30 Ils se réjouissent de ce qu'elles sont calmées; et il les conduit au port qu'ils désiraient.
Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
31 Qu'ils célèbrent la bonté de l'Éternel, et ses merveilles envers les fils des hommes!
Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
32 Qu'ils l'exaltent dans l'assemblée du peuple; qu'ils le louent dans le conseil des anciens!
Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
33 Il change les fleuves en désert, et les sources d'eaux en un sol aride;
Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
34 La terre fertile en lande salée, à cause de la méchanceté de ses habitants.
ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
35 Il change le désert en étang, et la terre aride en sources d'eaux.
Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
36 Il y fait habiter ceux qui étaient affamés; et ils fondent une ville pour l'habiter.
a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
37 Ils ensemencent des champs et plantent des vignes, qui rendent du fruit tous les ans.
Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
38 Il les bénit, et ils se multiplient extrêmement; il ne laisse point diminuer leur bétail.
ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
39 Puis, ils sont amoindris et humiliés par l'oppression, le malheur et la souffrance.
Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
40 Il répand le mépris sur les grands, et les fait errer dans un désert sans chemin.
shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
41 Mais il relève le pauvre de l'affliction, et rend les familles nombreuses comme des troupeaux.
Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
42 Les hommes droits le voient et s'en réjouissent; mais tous les injustes ont la bouche fermée.
Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
43 Que celui qui est sage prenne garde à ces choses, et considère les bontés de l'Éternel.
Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.

< Psaumes 107 >