< Proverbes 4 >
1 Enfants, écoutez l'instruction de votre père, et soyez attentifs pour connaître la prudence.
Ku saurara’ya’yana ga koyarwar mahaifinku; ku mai da hankali, ku sami fahimi.
2 Car je vous donne de bons conseils; n'abandonnez point mon enseignement.
Ina ba ku sahihiyar koyarwa, saboda haka kada ku ƙyale koyarwata.
3 Quand j'étais encore enfant près de mon père, tendre et chéri auprès de ma mère,
Sa’ad da nake yaro a gidan mahaifina, yaro kaɗai kuma na mahaifiyata,
4 Il m'enseignait et me disait: Que ton cœur retienne mes paroles; garde mes commandements, et tu vivras.
ya koya mini ya ce, “Ka riƙe kalmomina da dukan zuciyarka; ka kiyaye umarnaina za ka kuwa rayu.
5 Acquiers la sagesse, acquiers la prudence; ne l'oublie pas, et ne te détourne point des paroles de ma bouche.
Ka nemi hikima, ka nemi fahimi; kada ka manta da kalmomina ko ka kauce daga gare su.
6 Ne l'abandonne pas, elle te gardera; aime-la, et elle te protégera.
Kada ka ƙyale hikima, za tă kuwa tsare ka; ka ƙaunace ta, za tă kuwa lura da kai.
7 Le commencement de la sagesse, c'est d'acquérir la sagesse; acquiers la prudence au prix de tout ton avoir.
Hikima ce mafi girma duka; saboda haka ka nemi hikima. Ko da za tă ci duk abin da kake da shi, ka dai nemi fahimi.
8 Estime-la, et elle t'élèvera; elle fera ta gloire quand tu l'auras embrassée.
Ka ƙaunace ta, za tă ɗaukaka ka; ka rungume ta, za tă kuwa girmama ka.
9 Elle posera sur ta tête une couronne de grâces, et te donnera un diadème de gloire.
Za tă zama kayan ado da za su inganta kanka tă kuma zamar maka rawanin ɗaukaka.”
10 Écoute, mon fils, et reçois mes paroles; et les années de ta vie te seront multipliées.
Ka saurara, ɗana, ka yarda da abin da na faɗa, shekarun rayuwarka kuwa za su zama masu yawa.
11 Je t'ai enseigné le chemin de la sagesse, et je t'ai fait marcher dans les sentiers de la droiture.
Na bishe ka a hanyar hikima na kuma jagorance ka a miƙaƙƙun hanyoyi.
12 Quand tu marcheras, tes pas ne seront pas gênés, et quand tu courras, tu ne broncheras point.
Sa’ad da kake tafiya, ba abin da zai sa ka tuntuɓe; sa’ad da kake gudu, ba za ka fāɗi ba.
13 Embrasse l'instruction, ne la lâche point; garde-la, car c'est ta vie.
Ka riƙe umarni, kada ka bari yă kuɓuce; ka tsare shi sosai, gama ranka ne.
14 N'entre point dans le sentier des méchants, et ne pose pas ton pied dans le chemin des pervers.
Kada ka sa ƙafa a kan hanyar mugaye kada ka bi gurbin mugaye.
15 Détourne-t'en, ne passe point par là; écarte-toi, et passe outre.
Ka guji mugunta, kada ka yi tafiya a kanta; juya daga gare ta ka yi tafiyarka.
16 Car ils ne dormiraient pas, s'ils n'avaient fait quelque mal, et le sommeil leur serait ôté, s'ils n'avaient fait tomber personne.
Mugaye ba sa iya barci, sai sun aikata mugunta; ba su barci sai sun cuci wani.
17 Car ils mangent le pain de la méchanceté, et ils boivent le vin de la violence.
Mugunta da ta’adi kamar ci da sha suke a gare su.
18 Mais le sentier des justes est comme la lumière resplendissante, dont l'éclat augmente jusques à ce que le jour soit dans sa perfection.
Hanyar adali kamar fitowar rana ce, sai ƙara haske take yi, har ta kai tsaka.
19 La voie des méchants est comme l'obscurité; ils ne voient point ce qui les fera tomber.
Amma hanyar mugaye kamar zurfin duhu ne; ba sa sanin abin da ya sa suke tuntuɓe.
20 Mon fils, sois attentif à mes paroles, incline ton oreille à mes discours.
Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa, ka saurara sosai ga kalmomina.
21 Qu'ils ne s'éloignent pas de tes yeux, garde-les dans ton cœur.
Kada ka bari su rabu da kai, ka kiyaye su a cikin zuciyarka;
22 Car ils sont la vie de ceux qui les trouvent, et la santé de tout leur corps.
gama rai ne ga waɗanda suke nemansu da kuma lafiya ga dukan jikin mutum.
23 Garde ton cœur plus que toute autre chose qu'on garde; car c'est de lui que procèdent les sources de la vie.
Fiye da kome duka, ka tsare zuciyarka, gama maɓulɓulan ruwan rijiyar rai ne.
24 Éloigne de toi la perversité de la bouche, et la fausseté des lèvres.
Ka kau da muguwar magana daga bakinka; ka yi nesa da magana marar kyau daga leɓunanka.
25 Que tes yeux regardent droit, et que tes paupières se dirigent devant toi.
Bari idanunka su dubi gaba sosai, ka kafa idanunka kai tsaye a gabanka.
26 Balance le chemin de tes pieds, afin que toutes tes voies soient affermies.
Ka san inda ƙafafunka suke takawa ka bi hanyoyin da suke daram kawai.
27 Ne te détourne ni à droite ni à gauche; retire ton pied du mal.
Kada ka kauce dama ko hagu; ka kiyaye ƙafarka daga mugunta.