< Nombres 14 >

1 Alors toute l'assemblée éleva la voix, et se mit à jeter des cris, et le peuple pleura cette nuit-là.
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 Et tous les enfants d'Israël murmurèrent contre Moïse et contre Aaron, et toute l'assemblée leur dit: Que ne sommes-nous morts dans le pays d'Égypte ou dans ce désert! Que ne sommes-nous morts!
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 Et pourquoi l'Éternel nous conduit-il vers ce pays, pour y tomber par l'épée? Nos femmes et nos petits enfants y seront une proie. Ne vaudrait-il pas mieux pour nous, de retourner en Égypte?
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 Et ils se dirent l'un à l'autre: Établissons un chef, et retournons en Égypte.
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 Alors Moïse et Aaron tombèrent sur leurs visages, devant toute l'assemblée des enfants d'Israël.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 Et Josué, fils de Nun, et Caleb, fils de Jephunné, d'entre ceux qui avaient exploré le pays, déchirèrent leurs vêtements.
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 Et ils parlèrent à toute l'assemblée des enfants d'Israël, en disant: Le pays que nous avons parcouru pour l'explorer, est un fort bon pays.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 Si l'Éternel nous est favorable, il nous fera entrer dans ce pays, et nous le donnera; c'est un pays où coulent le lait et le miel.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 Seulement, ne vous révoltez point contre l'Éternel, et ne craignez point le peuple du pays; car ils seront notre pain; leur protection s'est retirée de dessus eux, et l'Éternel est avec nous; ne les craignez point.
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 Alors toute l'assemblée parla de les lapider; mais la gloire de l'Éternel apparut à tous les enfants d'Israël, sur le tabernacle d'assignation.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 Et l'Éternel dit à Moïse: Jusqu'à quand ce peuple me méprisera-t-il, et jusqu'à quand ne croiront-ils point en moi, malgré tous les signes que j'ai faits au milieu d'eux?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 Je le frapperai de mortalité, et je le détruirai; mais je te ferai devenir un peuple plus grand et plus fort qu'il n'est.
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 Et Moïse dit à l'Éternel: Mais les Égyptiens l'apprendront, car tu as fait monter ce peuple par ta force du milieu d'eux;
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 Et ils le diront aux habitants de ce pays. Ils ont entendu dire que tu es, ô Éternel, au milieu de ce peuple, et que tu apparais, ô Éternel, visiblement, que ta nuée se tient au-dessus d'eux, et que tu marches devant eux, le jour dans une colonne de nuée et la nuit dans une colonne de feu.
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 Et si tu fais mourir ce peuple, comme un seul homme, les nations qui ont entendu ta renommée, diront:
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 Parce que l'Éternel ne pouvait faire entrer ce peuple au pays qu'il avait juré de leur donner, il les a immolés dans le désert.
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 Or, maintenant, je te prie, que la puissance du Seigneur se montre dans sa grandeur, comme tu l'as déclaré, en disant:
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 L'Éternel est lent à la colère et abondant en grâce; il pardonne l'iniquité et le forfait; mais il ne tient point le coupable pour innocent; il punit l'iniquité des pères sur les enfants, jusqu'à la troisième et à la quatrième génération.
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Pardonne, je te prie, l'iniquité de ce peuple, selon la grandeur de ta grâce, et comme tu as pardonné à ce peuple depuis l'Égypte jusqu'ici.
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 Et l'Éternel dit: J'ai pardonné, selon ta parole.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 Mais aussi vrai que je suis vivant, et que la gloire de l'Éternel remplit toute la terre,
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 Tous les hommes qui ont vu ma gloire et les signes que j'ai faits en Égypte et au désert, et qui m'ont déjà tenté dix fois, et qui n'ont point écouté ma voix,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 Ne verront point le pays que j'ai promis par serment à leurs pères. Et tous ceux qui m'ont méprisé, ne le verront point.
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 Mais parce que mon serviteur Caleb a été animé d'un autre esprit, et m'a pleinement suivi, je le ferai entrer au pays où il est allé, et sa postérité le possédera.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 Or les Amalécites et les Cananéens habitent dans la vallée; retournez demain en arrière, et partez pour le désert dans la direction de la mer Rouge.
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 L'Éternel parla aussi à Moïse et à Aaron, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 Jusqu'à quand supporterai-je cette assemblée méchante, qui murmure contre moi? J'ai entendu les murmures que les enfants d'Israël murmurent contre moi.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Dis-leur: Aussi vrai que je suis vivant, dit l'Éternel, je vous ferai ce que j'ai entendu que vous avez dit;
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 Vos cadavres tomberont dans ce désert; et tous ceux d'entre vous qui ont été dénombrés, selon tout votre nombre, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, vous tous qui avez murmuré contre moi,
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 Vous n'entrerez pas au pays au sujet duquel j'ai levé ma main, jurant de vous y faire habiter; excepté Caleb, fils de Jephunné, et Josué, fils de Nun.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 Mais j'y ferai entrer vos petits enfants, dont vous avez dit qu'ils y seraient une proie; et ils connaîtront le pays que vous avez méprisé.
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 Mais vos cadavres, à vous, tomberont dans ce désert.
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 Et vos enfants iront paissant dans le désert quarante ans, et ils porteront la peine de vos prostitutions, jusqu'à ce que vos cadavres soient consumés dans le désert.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 D'après le nombre des jours pendant lesquels vous avez exploré le pays, savoir quarante jours, vous porterez la peine de vos iniquités pendant quarante ans, une année pour chaque jour, et vous connaîtrez l'effet de mon éloignement.
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 Moi, l'Éternel, je l'ai dit: Je ferai ceci à toute cette méchante assemblée, qui s'est réunie contre moi; ils seront consumés dans ce désert, et ils y mourront.
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 Et les hommes que Moïse avait envoyés pour explorer le pays, et qui étaient revenus et avaient fait murmurer contre lui toute l'assemblée, en décriant le pays;
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 Ces hommes, qui avaient décrié le pays, moururent frappés d'une plaie devant l'Éternel.
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 Mais Josué, fils de Nun, et Caleb, fils de Jephunné, survécurent, d'entre ces hommes qui étaient allés pour explorer le pays.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 Or Moïse dit ces paroles à tous les enfants d'Israël; et il y eut un grand deuil parmi le peuple.
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 Puis ils se levèrent de bon matin, et montèrent vers le sommet de la montagne, en disant: Nous voici, et nous monterons au lieu dont l'Éternel a parlé; car nous avons péché.
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 Mais Moïse dit: Pourquoi transgressez-vous le commandement de l'Éternel? Cela ne réussira point.
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 N'y montez pas, de peur que vous ne soyez battus devant vos ennemis, car l'Éternel n'est point au milieu de vous.
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 Car les Amalécites et les Cananéens sont là devant vous, et vous tomberez par l'épée, parce que vous vous êtes détournés de l'Éternel; et l'Éternel ne sera point avec vous.
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 Toutefois, ils s'obstinèrent à monter vers le sommet de la montagne; mais l'arche de l'alliance de l'Éternel et Moïse ne sortirent pas du milieu du camp.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 Et les Amalécites et les Cananéens, qui habitaient dans cette montagne, descendirent, et les battirent et les taillèrent en pièces jusqu'à Horma.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.

< Nombres 14 >