< Luc 2 >

1 En ce temps-là on publia un édit de César Auguste, pour faire le dénombrement des habitants de toute la terre.
A waɗancan kwanaki, Kaisar Augustus ya ba da doka cewa ya kamata a yi ƙidaya a dukan masarautar Roma.
2 Ce premier dénombrement se fit pendant que Quirinus était gouverneur de Syrie.
(Wannan ce ƙidaya ta fari da aka yi a lokacin da Kwiriniyus yake gwamnar Suriya.)
3 Ainsi tous allaient pour être enregistrés, chacun dans sa ville.
Sai kowa ya koma garinsa don a rubuta shi.
4 Joseph aussi monta de Galilée en Judée, de la ville de Nazareth à la ville de David, nommée Bethléhem, parce qu'il était de la maison et de la famille de David,
Saboda haka Yusuf ma ya haura daga Nazaret a Galili zuwa Yahudiya, ya tafi Betlehem garin Dawuda, don shi daga gida da kuma zuriyar Dawuda ne.
5 Pour être enregistré avec Marie son épouse, qui était enceinte.
Ya tafi can don a rubuta shi tare da Maryamu, wadda aka yi masa alkawari zai aura, tana kuwa da ciki.
6 Et pendant qu'ils étaient là, le temps auquel elle devait accoucher arriva.
Yayinda suke can, sai lokacin haihuwar jaririn ya yi,
7 Et elle mit au monde son fils premier-né, et elle l'emmaillota, et le coucha dans une crèche, parce qu'il n'y avait point de place pour eux dans l'hôtellerie.
ta kuwa haifi ɗanta na fari. Ta nannaɗe shi a zane ta kuma kwantar da shi cikin wani kwami, don ba su sami ɗaki a masauƙi ba.
8 Or, il y avait dans la même contrée des bergers qui couchaient aux champs, et qui gardaient leurs troupeaux pendant les veilles de la nuit.
Akwai makiyaya masu zama a fili kusa da wurin, suna tsaron garkunan tumakinsu da dare.
9 Et voici un ange du Seigneur se présenta à eux, et la gloire du Seigneur resplendit autour d'eux, et ils furent saisis d'une grande peur.
Sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, suka kuwa tsorata ƙwarai.
10 Alors l'ange leur dit: N'ayez point de peur; car je vous annonce une grande joie, qui sera pour tout le peuple;
Amma mala’ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Na kawo muku labari mai daɗi na farin ciki mai yawa ne wanda zai zama domin dukan mutane.
11 C'est qu'aujourd'hui, dans la ville de David, un Sauveur, qui est le Christ, le Seigneur, vous est né.
Yau a birnin Dawuda an haifa muku Mai Ceto; shi ne Kiristi Ubangiji.
12 Et ceci vous servira de signe: Vous trouverez le petit enfant emmailloté et couché dans une crèche.
Wannan zai zama alama a gare ku. Za ku tarar da jariri a nannaɗe a zane kwance a kwami.”
13 Et au même instant il y eut avec l'ange une multitude de l'armée céleste, louant Dieu et disant:
Ba labari sai ga taron rundunar sama suka bayyana tare da mala’ikan, suna yabon Allah suna cewa,
14 Gloire à Dieu, dans les lieux très hauts; paix sur la terre, bonne volonté envers les hommes!
“Ɗaukaka ga Allah a can cikin sama, a duniya kuma salama ga mutane waɗanda tagomashinsa yake bisansu.”
15 Et quand les anges se furent retirés d'avec eux dans le ciel, les bergers se dirent les uns aux autres: Allons donc jusqu'à Bethléhem, et voyons ce qui est arrivé, ce que le Seigneur nous a fait connaître.
Da mala’ikun suka bar su, su suka koma sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu je Betlehem mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar mana.”
16 Ils y allèrent donc en hâte, et trouvèrent Marie, et Joseph, et le petit enfant, qui était couché dans la crèche.
Sai suka tafi da sauri, suka tarar da Maryamu da Yusuf, da kuma jaririn kwance a kwami.
17 Et l'ayant vu, ils publièrent ce qui leur avait été dit touchant ce petit enfant.
Sa’ad da suka gan shi, sai suka baza maganar da aka gaya musu game da yaron,
18 Et tous ceux qui les entendirent, étaient dans l'admiration de ce que les bergers leur disaient.
duk kuwa waɗanda suka ji wannan, suka yi mamaki a kan abin da makiyayan suka faɗa.
19 Et Marie conservait toutes ces choses, les repassant dans son cœur.
Amma Maryamu ta riƙe dukan waɗannan abubuwa ta kuma yi ta tunaninsu a zuciyarta.
20 Et les bergers s'en retournèrent, glorifiant et louant Dieu de tout ce qu'ils avaient entendu et vu, conformément à ce qui leur avait été dit.
Makiyayan kuwa suka koma, suna ɗaukaka suna kuma yabon Allah saboda dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.
21 Quand les huit jours furent accomplis pour circoncire l'enfant, il fut appelé JÉSUS, nom qui lui avait été donné par l'ange, avant qu'il fût conçu dans le sein de sa mère.
A rana ta takwas, da lokaci ya yi da za a yi masa kaciya, sai aka ba shi suna Yesu, sunan da mala’ika ya ba shi kafin a yi cikinsa.
22 Et quand les jours de leur purification, selon la loi de Moïse, furent accomplis, on porta l'enfant à Jérusalem, pour le présenter au Seigneur,
Da lokacin tsarkakewarsu bisa ga Dokar Musa ya cika, sai Yusuf da Maryamu suka ɗauke shi suka haura zuwa Urushalima don su miƙa shi ga Ubangiji
23 Selon qu'il est écrit dans la loi du Seigneur: Tout mâle premier-né sera consacré au Seigneur; et pour offrir en sacrifice,
(yadda yake a rubuce a Dokar Ubangiji cewa, “Kowane ɗan fari, za a keɓe shi ga Ubangiji”),
24 Selon ce qui est prescrit dans la loi du Seigneur, une paire de tourterelles, ou deux pigeonneaux.
don kuma su miƙa hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Dokar Ubangiji cewa, “kurciyoyi biyu ko’yan tattabarai biyu.”
25 Il y avait à Jérusalem un homme qui s'appelait Siméon; cet homme était juste et pieux, il attendait la consolation d'Israël; et le Saint-Esprit était sur lui.
To, akwai wani mutum a Urushalima mai suna Siman, shi mai adalci da kuma mai ibada. Yana jiran fansar Isra’ila, Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi.
26 Et il avait été averti divinement par le Saint-Esprit qu'il ne mourrait point, qu'auparavant il n'eût vu le Christ du Seigneur.
An bayyana masa ta wurin Ruhu Mai Tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kiristi na Ubangiji.
27 Il vint au temple par l'Esprit, et comme le père et la mère apportaient le petit enfant Jésus, pour faire à son égard ce qui était en usage selon la loi,
Da Ruhu ya iza shi, sai ya shiga cikin filin haikali. Sa’ad da iyayen suka kawo jaririn nan Yesu don su yi masa abin da al’adar Doka ta bukaci,
28 Il le prit entre ses bras, et bénit Dieu, et dit:
sai Siman ya karɓi yaron a hannuwansa ya yabi Allah, yana cewa,
29 Seigneur, tu laisses maintenant aller ton serviteur en paix, selon ta parole;
“Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kamar yadda ka yi alkawari, yanzu ka sallami bawanka lafiya.
30 Car mes yeux ont vu ton salut,
Gama idanuna sun ga cetonka,
31 Que tu as préparé à la face de tous les peuples,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane,
32 La lumière qui doit éclairer les nations, et la gloire de ton peuple d'Israël.
haske don bayyanawa ga Al’ummai da kuma ɗaukaka ga mutanenka Isra’ila.”
33 Et Joseph et sa mère étaient dans l'admiration des choses qu'on disait de lui.
Mahaifin yaron da kuma mahaifiyarsa suka yi mamaki abin da aka faɗa game da shi.
34 Et Siméon les bénit, et dit à Marie sa mère: Voici, cet enfant est mis pour la chute et le relèvement de plusieurs en Israël, et pour être en butte à la contradiction;
Sa’an nan Siman ya sa musu albarka ya ce wa Maryamu mahaifiyarsa, “An ƙaddara yaron nan yă zama sanadin fāɗuwa da tashin mutane da yawa a Isra’ila, zai kuma zama alamar da mutane ba za su so ba,
35 En sorte que les pensées du cœur de plusieurs seront découvertes; et pour toi une épée te transpercera l'âme.
ta haka za a fallasa tunanin zukatan mutane da yawa. Ke ma, takobi zai soki zuciyarki.”
36 Il y avait aussi Anne la prophétesse, fille de Phanuel, de la tribu d'Ascer; elle était fort avancée en âge, et elle avait vécu avec son mari, sept ans, depuis sa virginité.
Akwai wata annabiya ma, mai suna Anna, diyar Fanuwel, na kabilar Asher. Ta tsufa kutuf; ta yi zama da mijinta shekaru bakwai bayan sun yi aure,
37 Elle était veuve, âgée d'environ quatre-vingt-quatre ans, et elle ne sortait point du temple, servant Dieu nuit et jour en jeûnes et en prières.
ta kuwa zama gwauruwa sai da ta kai shekaru tamanin da huɗu. Ba ta taɓa barin haikali ba, tana sujada dare da rana, tana kuma azumi da addu’a.
38 Étant survenue à cette heure, elle louait aussi le Seigneur, et elle parlait de Jésus à tous ceux de Jérusalem qui attendaient la délivrance d'Israël.
Tana haurawa wurinsu ke nan a wannan lokaci, sai ta yi wa Allah godiya ta kuma yi magana game da yaron nan ga dukan waɗanda suke sauraron fansar Urushalima.
39 Et après qu'ils eurent accompli tout ce qui est ordonné par la loi du Seigneur, ils retournèrent en Galilée, à Nazareth, leur ville.
Bayan da Yusuf da Maryamu suka gama yin dukan abubuwan da Dokar Ubangiji ta bukaci, sai suka koma Galili suka tafi Nazaret garinsu.
40 Et l'enfant croissait et se fortifiait en esprit, étant rempli de sagesse; et la grâce de Dieu était sur lui.
Yaron kuwa ya yi girma ya yi ƙarfi; ya cika da hikima, alherin Allah kuwa yana bisansa.
41 Or, son père et sa mère allaient tous les ans à Jérusalem, à la fête de Pâque.
Kowace shekara, iyayen Yesu sukan je Urushalima don Bikin Ƙetarewa.
42 Et quand il eut douze ans, ils montèrent à Jérusalem, selon la coutume de la fête.
Da Yesu ya cika shekaru goma sha biyu, sai suka tafi Bikin bisa ga al’ada.
43 Lorsque les jours de la fête furent achevés, comme ils s'en retournaient, l'enfant Jésus resta à Jérusalem;
Bayan Bikin, da iyayen suka kama hanya don su koma gida, sai Yesu, yaron nan, ya tsaya a Urushalima, ba da saninsu ba.
44 Et Joseph et sa mère ne s'en aperçurent point. Mais, pensant qu'il était avec leurs compagnons de voyage, ils marchèrent une journée, puis ils le cherchèrent parmi leurs parents et ceux de leur connaissance;
Su kuwa sun ɗauka yana tare da su, saboda haka, suka yi ta tafiya har na yini guda. Sa’an nan suka fara nemansa cikin’yan’uwansu da abokansu.
45 Et ne le trouvant point, ils retournèrent à Jérusalem pour le chercher.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima nemansa.
46 Et au bout de trois jours ils le trouvèrent dans le temple, assis au milieu des docteurs, les écoutant et leur faisant des questions.
Bayan kwana uku, sai suka same shi a filin haikali zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu yana kuma yi musu tambayoyi.
47 Et tous ceux qui l'entendaient, étaient ravis de sa sagesse et de ses réponses.
Dukan waɗanda suka ji shi, suka yi mamakin fahimtarsa, da amsoshinsa.
48 Quand ses parents le virent, ils furent étonnés; et sa mère lui dit: Mon enfant, pourquoi as-tu ainsi agi avec nous? Voici ton père et moi, nous te cherchions, étant fort en peine.
Da iyayensa suka gan shi sai suka yi mamaki. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, don me ka yi mana haka? Ni da mahaifinka duk mun damu muna nemanka.”
49 Et il leur dit: Pourquoi me cherchiez-vous? Ne saviez-vous pas qu'il me faut être occupé aux affaires de mon Père?
Sai ya ce, “Don me kuke nemana? Ba ku san cewa, dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 Mais ils ne comprirent point ce qu'il leur disait.
Amma ba su fahimci abin da yake faɗin musu ba.
51 Il s'en alla ensuite avec eux, et vint à Nazareth, et il leur était soumis. Et sa mère conservait toutes ces choses dans son cœur.
Sai ya koma Nazaret tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuma ta riƙe dukan waɗannan abubuwa a zuciyarta.
52 Et Jésus croissait en sagesse, en stature et en grâce, devant Dieu et devant les hommes.
Yesu kuwa ya yi girma, ya kuma ƙaru cikin hikima, ya kuma sami tagomashi a wurin Allah da mutane.

< Luc 2 >