< Job 8 >
1 Alors Bildad, de Shuach, prit la parole, et dit:
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 Jusques à quand parleras-tu ainsi, et les paroles de ta bouche ressembleront-elles à un vent impétueux?
“Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
3 Dieu ferait-il fléchir le droit, le Tout-Puissant ferait-il fléchir la justice?
Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
4 Si tes fils ont péché contre lui, il les a livrés à leur crime.
Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
5 Mais toi, si tu cherches Dieu, et si tu demandes grâce au Tout-Puissant,
Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
6 Si tu es pur et droit, il veillera certainement sur toi; il restaurera la demeure de ta justice;
in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
7 Tes commencements auront été peu de chose, et ta fin sera très grande.
Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
8 Interroge, en effet, les générations précédentes, et fais attention aux recherches de leurs pères;
“Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
9 Car nous sommes d'hier et nous ne savons rien; car nos jours sur la terre sont comme une ombre;
gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
10 Mais eux, ne t'enseigneront-ils pas, ne te parleront-ils pas, ne tireront-ils pas de leur cœur ces discours:
Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
11 Le roseau croît-il hors des marais, et le jonc pousse-t-il sans eau?
Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
12 Il est encore en sa verdure, on ne le coupe pas, et avant toutes les herbes, il est desséché.
Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
13 Telle est la destinée de tous ceux qui oublient Dieu: l'espérance de l'impie périra.
Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
14 Sa confiance sera trompée, et sa sécurité deviendra une toile d'araignée;
Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
15 Il s'appuiera sur sa maison, et elle ne tiendra pas; il s'y cramponnera, et elle ne restera pas debout.
Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
16 Il est plein de vigueur, exposé au soleil, et ses jets poussent par-dessus son jardin;
Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
17 Mais ses racines s'entrelacent sur des monceaux de pierres, il rencontre un sol de rochers,
shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
18 Et si on l'enlève de sa place, celle-ci le renie et lui dit: Je ne t'ai point connu!
Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
19 Telle est la joie qu'il a de sa conduite, et d'autres après lui s'élèveront de la poussière.
Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
20 C'est ainsi que Dieu ne rejette pas l'homme intègre, mais il ne donne pas la main aux méchants.
“Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
21 Il remplira encore ta bouche de joie, et tes lèvres de chants d'allégresse.
Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
22 Tes ennemis seront couverts de honte, et la tente des méchants ne sera plus!
Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”