< Job 40 >

1 L'Éternel adressa la parole à Job, et dit:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Le censeur contestera-t-il avec le Tout-Puissant? L'accusateur de Dieu répondra-t-il à cela?
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Alors Job répondit à l'Éternel et dit:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Je suis trop peu de chose; que te répondrais-je? Je mets ma main sur ma bouche.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 J'ai parlé une fois, et je ne répondrai plus. J'ai parlé deux fois, et je n'y retournerai plus.
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Et l'Éternel répondit à Job du sein de la tempête, et dit:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Ceins tes reins, comme un vaillant homme; je t'interrogerai, et tu m'instruiras.
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Est-ce que tu voudrais anéantir ma justice? me condamner pour te justifier?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 As-tu un bras comme celui de Dieu; tonnes-tu de la voix, comme lui?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Pare-toi donc de magnificence et de grandeur; et revêts-toi de majesté et de gloire.
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Répands les fureurs de ta colère, d'un regard humilie tous les orgueilleux;
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 D'un regard abaisse tous les orgueilleux, et écrase les méchants sur place.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Cache-les tous ensemble dans la poussière, et enferme leurs visages dans les ténèbres.
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 Alors, moi aussi, je te louerai, car ta main t'aura aidé.
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Vois donc le Béhémoth, que j'ai fait aussi bien que toi; il mange l'herbe comme le bœuf;
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Vois donc: sa force est dans ses flancs, et sa vigueur dans les muscles de son ventre.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Il remue sa queue semblable au cèdre; les tendons de ses hanches sont entrelacés.
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Ses os sont des tubes d'airain, ses membres sont comme des barres de fer.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 C'est le chef-d'œuvre de Dieu, son créateur lui a donné son épée.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Les montagnes portent pour lui leur herbe; là se jouent toutes les bêtes des champs.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Il se couche sous les lotus, dans l'ombre des roseaux et dans le limon.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Les lotus le couvrent de leur ombre, et les saules du torrent l'environnent.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Vois, le fleuve déborde avec violence, il n'a point peur; il serait tranquille quand le Jourdain monterait à sa gueule.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Qu'on le prenne à force ouverte! Ou qu'à l'aide de filets on lui perce le nez!
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Job 40 >