< Job 14 >

1 L'homme né de femme a la vie courte, et est rassasié de trouble.
“Mutum haihuwar mace kwanakinsa kaɗan ne, kuma cike da wahala.
2 Comme une fleur, il éclot, et on le coupe; il fuit comme une ombre, et ne subsiste point.
Yana tasowa kamar fure yana kuma shuɗewa; kamar inuwa, ba ya daɗewa.
3 Et c'est sur cet être que tu ouvres les yeux, et c'est moi que tu conduis en justice avec toi!
Za ka zura ido a kan irin wannan ne? Za ka kawo shi gaba don ka yi masa shari’a?
4 Qui peut tirer la pureté de la souillure? Personne.
Wane ne zai iya kawo abin da yake da tsarki daga cikin abu marar tsarki? Babu!
5 Si ses jours sont déterminés, si le nombre de ses mois est fixé par-devers toi, si tu lui as prescrit des limites qu'il ne passera pas,
An lissafta kwanakin mutum; ka riga ka ɗibar masa watanni, ka yi masa iyaka, ba zai iya wuce iyakar ba.
6 Détourne tes regards de lui, et qu'il ait quelque repos, jusqu'à ce qu'il goûte, comme un mercenaire, la fin de sa journée.
Saboda haka ka kawar da kanka daga gare shi, ka rabu da shi har sai ya cika lokacinsa kamar mutumin da aka ɗauki hayarsa.
7 Car il y a de l'espérance pour l'arbre, si on l'a coupé; il reverdit encore, et il ne cesse pas d'avoir des rejetons;
“Aƙalla itace yana da bege. In an sare shi, zai sāke tsira, zai tohu da kyau.
8 Si sa racine vieillit dans la terre, et si dans la poussière son tronc est mort,
Ko da jijiyoyin itacen sun tsufa a cikin ƙasa kuma kututturensa ya mutu a cikin ƙasa.
9 Dès qu'il sent l'eau, il pousse de nouveau, et il produit des branches comme un jeune plant.
Daga ya ji ƙanshin ruwa zai tohu yă yi tsiro kamar shuka.
10 Mais quand l'homme meurt, il reste gisant; quand l'homme a expiré, où est-il?
Amma mutum yana mutuwa a bizne shi; daga ya ja numfashinsa na ƙarshe, shi ke nan.
11 Les eaux de la mer s'écoulent, le fleuve tarit et se dessèche,
Kamar yadda ruwa yake bushewa a teku ko a gaɓar rafi sai wurin yă bushe,
12 Ainsi l'homme se couche, et il ne se relève point. Tant qu'il y aura des cieux, ils ne se réveilleront point, et on ne les fera pas sortir de leur sommeil.
haka mutum zai kwanta ba zai tashi ba; har sai duniya ta shuɗe mutane ba za su farka ba, ba za su tashi daga barcinsu ba.
13 Oh! si tu me cachais dans le Sépulcre, si tu me mettais à couvert, jusqu'à ce que ta colère fût passée! Si tu me donnais un terme, après lequel tu te souviendrais de moi (Sheol h7585)
“Da ma za ka ɓoye ni a cikin kabari ka ɓoye ni har sai fushinka ya wuce! In da za ka keɓe mini lokaci sa’an nan ka tuna da ni! (Sheol h7585)
14 (Si l'homme meurt, revivra-t-il? ), tout le temps de ma consigne, j'attendrais, jusqu'à ce que vînt mon remplacement!
In mutum ya mutu, ko zai sāke rayuwa? In haka ne zan daure kwanakin da nake shan wahala har su wuce.
15 Tu appellerais, et je répondrais; tu désirerais de revoir l'ouvrage de tes mains.
Za ka kira zan kuwa amsa maka; za ka yi marmarin abin da hannunka ya halitta.
16 Mais, maintenant, tu comptes mes pas, et tu observes tous mes péchés.
Ba shakka a lokacin ne za ka lura da matakaina amma ba za ka kula da zunubaina ba.
17 Ma transgression est scellée dans le sac, et tu as ajouté à mon iniquité.
Za a daure laifofina a cikin jaka; za ka rufe zunubaina.
18 Mais la montagne s'éboule; le rocher est transporté hors de sa place;
“Amma kamar yadda manyan duwatsu suke fāɗuwa su farfashe su kuma gusa daga wurarensu,
19 Les eaux minent les pierres; les inondations entraînent la poussière de la terre: ainsi fais-tu périr l'espérance du mortel.
yadda ruwa yakan zaizaye duwatsu ruwa mai ƙarfi kuma yă kwashe turɓayar ƙasa, haka kake barin mutum ba bege.
20 Tu ne cesses de l'assaillir, et il s'en va; tu changes son aspect, et tu le renvoies.
Ka sha ƙarfinsa gaba ɗaya, sai ya ɓace, ka sauya yanayinsa ka kuma kore shi.
21 Que ses fils soient honorés, il n'en saura rien; qu'ils soient méprisés, il ne le verra pas.
Ko an martaba’ya’yansa maza, ba zai sani ba; Ko an wulaƙanta su, ba zai gani ba.
22 C'est sur lui seul que sa chair s'afflige, et sur lui que son âme gémit.
Zafin jikinsa kaɗai yake ji yana kuka wa kansa ne kaɗai.”

< Job 14 >