< Job 11 >

1 Alors Tsophar, de Naama, prit la parole, et dit:
Sa’an nan Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 Ne répondra-t-on point à tant de discours, et suffira-t-il d'être un grand parleur pour être justifié?
“Duk surutun nan ba za a amsa maka ba? Ko mai surutun nan marar laifi ne?
3 Tes vains propos feront-ils taire les gens? Te moqueras-tu, sans que personne te confonde?
Ko maganganun nan naka marasa amfani za su sa mutane su yi maka shiru? Ba wanda zai kwaɓe ka lokacin da kake faɗar maganar da ba daidai ba?
4 Tu as dit: Ma doctrine est pure, je suis sans tache devant tes yeux.
Ka ce wa Allah, ‘Abin da na gaskata ba laifi ba ne kuma ni mai tsabta ne a gabanka.’
5 Mais je voudrais que Dieu parlât, et qu'il ouvrît sa bouche pour te répondre;
Da ma Allah zai yi magana, yă buɗe baki yă faɗi wani abin da ka yi da ba daidai ba
6 Qu'il te montrât les secrets de sa sagesse, de son immense sagesse; et tu reconnaîtrais que Dieu oublie une partie de ton iniquité.
yă kuma buɗe maka asirin hikima, gama hikima ta gaskiya tana da gefe biyu. Ka san wannan, Allah ya riga ya manta da waɗansu zunubanka.
7 Trouveras-tu le fond de Dieu? Trouveras-tu la limite du Tout-Puissant?
“Ko za ka iya gane al’amuran Allah? Ko za ka iya gane girman asirin Maɗaukaki?
8 Ce sont les hauteurs des cieux: qu'y feras-tu? C'est plus profond que les enfers: qu'y connaîtras-tu? (Sheol h7585)
Sun fi nisan sama tudu, me za ka iya yi? Sun fi zurfin kabari zurfi, me za ka sani? (Sheol h7585)
9 Son étendue est plus longue que la terre, et plus large que la mer.
Tsayinsu ya fi tsawon duniya da kuma fāɗin teku.
10 S'il saisit, s'il emprisonne, s'il assemble le tribunal, qui l'en empêchera?
“In ya zo ya kulle ka a kurkuku ya ce kai mai laifi ne, wa zai hana shi?
11 Car il connaît, lui, les hommes de rien; il voit l'iniquité, sans qu'elle s'en doute;
Ba shakka yana iya gane mutanen da suke marasa gaskiya; kuma in ya ga abin da yake mugu, ba ya kula ne?
12 Mais l'homme vide de sens de-viendra intelligent, quand l'ânon sauvage naîtra comme un homme!
Amma daƙiƙin mutum ba ya taɓa zama mai hikima kamar dai a ce ba a taɓa haihuwar ɗan aholaki horarre.
13 Si tu disposes bien ton cœur, et si tu étends tes mains vers Dieu,
“Duk da haka in ka miƙa masa zuciyarka, ka kuma miƙa hannuwanka gare shi,
14 (Si l'iniquité est en tes mains, éloigne-la, et que le crime n'habite point dans tes tentes! )
in ka kawar da zunubin da yake hannunka, ba ka bar zunubi ya kasance tare da kai ba
15 Alors certainement tu lèveras ton front sans tache; tu seras raffermi et tu ne craindras rien;
shi ne za ka iya ɗaga fuskarka ba tare da jin kunya ba; za ka tsaya da ƙarfi kuma ba za ka ji tsoro ba.
16 Tu oublieras tes peines, tu t'en souviendras comme des eaux écoulées.
Ba shakka za ka manta da wahalolinka, za ka tuna da su kamar yadda ruwa yake wucewa.
17 La vie se lèvera pour toi plus brillante que le midi, et l'obscurité même sera comme le matin.
Rayuwarka za tă fi hasken rana haske, duhu kuma zai zama kamar safiya.
18 Tu seras plein de confiance, parce que tu auras lieu d'espérer; tu exploreras autour de toi, et tu te coucheras en sécurité;
Za ka zauna lafiya, domin akwai bege; za ka duba kewaye da kai ka huta cikin kwanciyar rai.
19 Tu t'étendras à ton aise, et nul ne t'effraiera; et bien des gens te feront la cour.
Za ka kwanta, ba wanda zai sa ka ji tsoro, da yawa za su zo neman taimako a wurinka.
20 Mais les yeux des méchants seront consumés; tout refuge leur sera ôté, et toute leur espérance sera de rendre l'âme.
Amma idanun mugaye ba za su iya gani ba, kuma ba za su iya tserewa ba; begensu zai zama na mutuwa.”

< Job 11 >