< Jérémie 49 >

1 Pour les enfants d'Ammon. Ainsi a dit l'Éternel: Israël n'a-t-il point de fils? N'a-t-il point d'héritier? Pourquoi Malcam hérite-t-il de Gad, et son peuple habite-t-il dans ses villes?
Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
2 C'est pourquoi les jours viennent, dit l'Éternel, où je ferai entendre le cri de guerre vers Rabba des enfants d'Ammon; elle deviendra un monceau de ruines, et les villes de son ressort seront consumées par le feu, et Israël possédera ceux qui l'auront possédé, a dit l'Éternel.
Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
3 Hurle, Hesbon! car Haï est saccagée; filles de Rabba, criez, revêtez-vous de sacs, lamentez-vous, courez çà et là le long des murailles. Car Malcam ira en captivité, avec ses sacrificateurs et ses chefs.
“Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
4 Pourquoi te glorifies-tu de tes vallées? Le sang coulera dans ta vallée, fille infidèle, qui te confies dans tes trésors et dis: Qui viendra contre moi?
Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
5 Voici, je vais faire venir de tous tes environs la terreur contre toi, dit le Seigneur, l'Éternel des armées; et vous serez chassés chacun devant soi, et personne ne rassemblera les fugitifs.
Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
6 Mais, après cela, je ramènerai les captifs des enfants d'Ammon, dit l'Éternel.
“Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
7 Pour Édom. Ainsi a dit l'Éternel des armées: N'y a-t-il plus de sagesse dans Théman? Le conseil manque-t-il aux hommes entendus? Leur sagesse s'est-elle évanouie?
Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
8 Fuyez, tournez le dos, prenez des cavernes pour demeures, habitants de Dédan! car je fais venir sur Ésaü sa calamité, le temps auquel je veux le visiter.
Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
9 Si des vendangeurs entraient chez toi, ne laisseraient-ils pas des grappillages? Si c'étaient des voleurs de nuit, ils ne prendraient que ce qui leur suffit.
In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
10 Mais moi, j'ai dépouillé Ésaü, j'ai découvert ses retraites, il ne peut plus se cacher; sa postérité, ses frères, ses voisins sont dévastés, et il n'est plus.
Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
11 Laisse tes orphelins; je les ferai vivre; et que tes veuves s'assurent en moi!
Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
12 Car ainsi a dit l'Éternel: Voici, ceux qui ne devaient pas boire la coupe la boiront, et toi, en serais-tu exempt? Tu n'en seras pas exempt; mais tu la boiras certainement.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
13 Car j'ai juré par moi-même, dit l'Éternel, que Botsra sera réduite en désolation, en opprobre, en désert et en malédiction, et que toutes ses villes deviendront des solitudes éternelles.
Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
14 Je l'ai entendu de la part de l'Éternel: Un messager est envoyé parmi les nations: “Assemblez-vous, dit-il, et venez contre elle, et levez-vous pour combattre! “
Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
15 Car voici, je te rendrai petite entre les nations, et méprisée entre les hommes.
“Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
16 Ta présomption, l'orgueil de ton cœur t'a séduite, toi qui habites le creux des rochers et qui occupes le sommet des collines. Quand tu élèverais ton nid comme l'aigle, je te précipiterai de là, dit l'Éternel.
Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
17 Et l'Idumée sera réduite en désolation; tellement que quiconque passera près d'elle en sera étonné, et sifflera à cause de toutes ses plaies.
“Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
18 Comme dans la destruction de Sodome et de Gomorrhe, et des villes voisines, a dit l'Éternel, il n'y habitera personne et aucun fils d'homme n'y séjournera.
Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
19 Voici, tel qu'un lion, il monte des bords orgueilleux du Jourdain vers la demeure forte. Car, en un moment, je le ferai courir sur elle, et je donnerai mission contre elle à celui que j'ai choisi. Car qui est semblable à moi? Qui m'assignera? Et quel est le berger qui me résistera?
“Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
20 C'est pourquoi, écoutez la résolution que l'Éternel a prise contre Édom, et les desseins qu'il a formés contre les habitants de Théman: Certainement on les traînera comme les plus petits du troupeau! Certainement on détruira sur eux leurs demeures!
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
21 Au bruit de leur chute, la terre tremble, et la voix de leur cri se fait entendre jusqu'à la mer Rouge.
Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
22 Voici, il monte comme l'aigle, il vole, il étend ses ailes sur Botsra, et en ce jour-là le cœur des héros d'Édom sera comme le cœur d'une femme en travail.
Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
23 Pour Damas. Hamath et Arpad sont confondues; car elles ont appris de fâcheuses nouvelles; elles défaillent! C'est comme la mer par une tourmente; elle ne peut s'apaiser.
Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
24 Damas n'a plus de force; elle se tourne pour fuir; la peur s'empare d'elle; l'angoisse et les douleurs la saisissent comme celle qui enfante.
Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 Comment n'est-elle point abandonnée, la ville fameuse, la cité de ma joie?
Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
26 C'est pourquoi ses jeunes gens tomberont dans ses rues, et tous les hommes de guerre périront en ce jour-là, dit l 'Éternel des armées.
Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
27 Et je mettrai le feu dans les murs de Damas, et il dévorera les palais de Ben-Hadad.
“Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
28 Pour Kédar et les royaumes de Hatsor, que frappa Nébucadnetsar, roi de Babylone. Ainsi a dit l'Éternel: Levez-vous, montez vers Kédar, et détruisez les enfants de l'Orient.
Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
29 On enlèvera leurs tentes et leurs troupeaux; on s'emparera de leurs tapis, de tous leurs bagages et de leurs chameaux, et on criera: “Frayeur de tous côtés! “
Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
30 Fuyez! Éloignez-vous tant que vous pourrez! Prenez dans les creux vos demeures, habitants de Hatsor! dit l'Éternel; car Nébucadnetsar, roi de Babylone, a formé contre vous un dessein, il a pris une résolution contre vous.
“Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
31 Levez-vous; montez vers une nation qui est en repos et qui habite en assurance, dit l'Éternel. Ils n'ont ni portes, ni barres; ils habitent seuls.
“Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
32 Leurs chameaux seront au pillage, et la multitude de leur bétail sera une proie. Je les disperserai à tout vent, ces gens qui se rasent les coins de la barbe, et je ferai venir leur calamité de tous les côtés, dit l'Éternel.
Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
33 Et Hatsor deviendra un repaire de chacals et un désert à toujours. Il n'y demeurera personne, et aucun fils d'homme n'y séjournera!
“Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
34 La parole de l'Éternel qui fut adressée à Jérémie, le prophète, touchant Élam, au commencement du règne de Sédécias, roi de Juda, en ces termes:
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
35 Ainsi a dit l'Éternel des armées: Voici, je vais rompre l'arc d'Élam, leur principale force.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
36 Et je ferai venir contre Élam, les quatre vents, des quatre extrémités des cieux; et je les disperserai par tous ces vents-là, et il n'y aura pas de nation où ne viennent des fugitifs d'Élam.
Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
37 Je ferai que les Élamites seront épouvantés devant leurs ennemis et devant ceux qui cherchent leur vie; et j'amènerai sur eux le malheur, l'ardeur de ma colère, dit l'Éternel; et j'enverrai après eux l'épée, jusqu'à ce que je les aie consumés.
Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
38 Et je placerai mon trône dans Élam, et j'en détruirai les rois et les chefs, dit l'Éternel.
Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
39 Mais il arrivera qu'aux derniers jours je ramènerai les captifs d'Élam, dit l'Éternel.
“Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.

< Jérémie 49 >