< Jérémie 34 >
1 La parole qui fut adressée en ces mots à Jérémie, de la part de l'Éternel, lorsque Nébucadnetsar, roi de Babylone, et toute son armée, tous les royaumes de la terre gouvernés par sa main, et tous les peuples, combattaient contre Jérusalem et contre toutes ses villes:
Yayinda Nebukadnezzar sarkin Babilon da dukan sojojinsa da kuma dukan mulkokinsa da mutanen masarautar da yake mulki suna yaƙi da Urushalima da dukan garuruwan da suke kewaye, sai wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Ainsi a dit l'Éternel, le Dieu d'Israël: Va, et parle à Sédécias, roi de Juda, et dis-lui: Ainsi a dit l'Éternel: Voici, je vais livrer cette ville dans la main du roi de Babylone, et il la brûlera.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi wurin Zedekiya sarkin Yahuda ka faɗa masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ina gab da ba da wannan birni ga sarkin Babilon, zai kuwa ƙone ta.
3 Et toi, tu n'échapperas pas à sa main; car certainement tu seras pris, et tu seras livré entre ses mains; et tes yeux verront les yeux du roi de Babylone, et il te parlera bouche à bouche, et tu iras à Babylone.
Ba za ka tsere daga hannunsa ba amma tabbatacce za a kama ka a kuma ba da kai gare shi. Za ka ga sarkin Babilon da idanunka, zai kuwa yi magana da kai fuska da fuska. Za ka kuwa tafi Babilon.
4 Toutefois, écoute la parole de l'Éternel, Sédécias, roi de Juda! Ainsi a dit l'Éternel: Tu ne mourras point par l'épée.
“‘Duk da haka ka ji alkawarin Ubangiji, ya Zedekiya sarkin Yahuda. Ga abin da Ubangiji yake cewa game da kai. Ba za ka mutu ta takobi ba;
5 Tu mourras en paix, et comme on a brûlé des parfums pour tes pères, les rois précédents qui ont été avant toi, on en brûlera pour toi et on te pleurera, en disant: Hélas, Seigneur! Car j'ai prononcé cette parole, dit l'Éternel.
za ka mutu cikin salama. Yadda mutane suka ƙuna wutar jana’iza don girmama kakanninka, sarakunan da suka riga ka, haka za su ƙuna wuta don girmama da kuma makokinka suna cewa, “Kaito, ya maigida!” Ni kaina na yi wannan alkawari, in ji Ubangiji.’”
6 Jérémie, le prophète, prononça toutes ces paroles à Sédécias, roi de Juda, à Jérusalem.
Sa’an nan annabi Irmiya ya faɗi dukan wannan wa Zedekiya sarkin Yahuda, a Urushalima,
7 Et l'armée du roi de Babylone combattait contre Jérusalem et contre toutes les villes de Juda qui restaient, contre Lakis et contre Azéka; car c'étaient les villes fortes qui restaient d'entre les villes de Juda.
yayinda sojojin sarkin Babilon suna yaƙi da Urushalima da sauran garuruwan Yahuda waɗanda suka ragu, Lakish da Azeka. Waɗannan su ne birane masu katanga kaɗai a Yahuda.
8 La parole qui fut adressée par l'Éternel à Jérémie, après que le roi Sédécias eut fait une alliance avec tout le peuple de Jérusalem, pour proclamer la liberté parmi eux,
Maganar ta zo wa Irmiya daga Ubangiji bayan Sarki Zedekiya ya yi yarjejjeniya da duka mutane a Urushalima ya yi shelar’yanci wa bayi.
9 Afin que chacun renvoyât libre son serviteur israélite et chacun sa servante israélite, et que personne ne rendît esclave le Juif, son frère.
Kowa ya’yantar da bayinsa da suke Ibraniyawa, maza da mata; kada kowa ya riƙe bawa wanda yake mutumin Yahuda.
10 Tous les chefs et tout le peuple qui étaient entrés dans cette alliance, s'engagèrent à renvoyer libres chacun son serviteur et chacun sa servante, sans plus les tenir dans l'esclavage. Ils obéirent et les renvoyèrent.
Saboda haka dukan fadawa da mutane suka yi yarjejjeniyar cewa za su’yantar da bayinsu maza da mata ba za su kuwa ƙara riƙe su bayi ba. Suka yarda, suka kuma sake su.
11 Mais ensuite ils changèrent d'avis, et firent revenir leurs serviteurs et leurs servantes, qu'ils avaient renvoyés libres, et se les assujettirent comme serviteurs et comme servantes.
Amma daga baya suka canja ra’ayoyinsu suka maido bayinsu suka kuma sāke bautar da su.
12 Alors la parole de l'Éternel fut adressée à Jérémie, en ces mots:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Ainsi a dit l'Éternel le Dieu d'Israël: J'ai fait alliance avec vos pères au jour où je les tirai hors du pays d'Égypte, de la maison de servitude, et je leur ai dit:
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa na yi alkawari da kakanni-kakanninku sa’ad da na fitar da su daga Masar, daga ƙasar bauta. Na ce,
14 Au bout de sept ans, vous renverrez chacun votre frère hébreu qui vous aura été vendu. Il te servira six ans: puis tu le renverras libre de chez toi. Mais vos pères ne m'ont point écouté et n'ont point prêté l'oreille.
‘A kowace shekara ta bakwai dole kowannenku yă’yantar da duk wani ɗan’uwa mutumin Ibraniyawa wanda aka sayar masa. Bayan ya yi muku hidima shekaru shida, dole ku bar shi yă tafi’yantacce.’ Amma kakanninku ba su saurare ni ba, ba su ji ni ba.
15 Cependant vous étiez revenus aujourd'hui; vous aviez fait ce qui est droit à mes yeux, en publiant chacun la liberté de son prochain; et vous aviez traité l'alliance en ma présence, dans la maison sur laquelle mon nom est invoqué.
Bai daɗe ba da kuka tuba, kuka kuma yi abin da yake mai kyau a idona. Kowannenku ya yi shelar’yanci ga ɗan’uwansa. Kun ma yi yarjejjeniya a gabana a gidan da ake kira da Sunana.
16 Mais vous avez changé d'avis, et vous avez profané mon nom, en faisant revenir chacun son serviteur et chacun sa servante, que vous aviez renvoyés libres et pour être à eux-mêmes; et vous les avez forcés à être vos serviteurs et vos servantes.
Amma yanzu kun juya kun kuma ɓata sunana; kowannenku ya mayar da bayi maza da matan da kuka’yantar su tafi inda suka ga dama. Kun sāke tilasta su su zama bayinku.
17 C'est pourquoi ainsi a dit l'Éternel: Vous ne m'avez point obéi, pour publier la liberté, chacun à son frère, chacun à son prochain; voici, dit l'Éternel, je publie la liberté contre vous à l'épée, à la peste et à la famine, et je vous livrerai pour être agités par tous les royaumes de la terre.
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa, kun yi mini rashin biyayya; ba ku yi shelar’yanci don’yan’uwanku ba. Saboda haka yanzu na yi muku shelar’yanci in ji Ubangiji,’yanci ga mutuwa ta takobi, annoba da kuma yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga sauran mulkokin duniya.
18 Et je livrerai les hommes qui ont transgressé mon alliance, qui n'ont pas exécuté les paroles de l'accord qu'ils avaient fait devant moi, en passant entre les deux moitiés du veau qu'ils avaient coupé en deux,
Mutanen da suka keta alkawarina da ba su cika sharuɗan alkawarin da suka yi a gabana ba, zan yi da su kamar ɗan maraƙin da suka yanka biyu suka bi ta tsakiyarsa.
19 Les chefs de Juda et les chefs de Jérusalem, les eunuques et les sacrificateurs, et tous les gens du pays qui ont passé entre les moitiés du veau,
Shugabannin Yahuda da Urushalima, fadawa, firistoci da kuma dukan mutanen ƙasar waɗanda suka bi tsakanin ɗan maraƙin da aka yanka,
20 Je les livrerai entre les mains de leurs ennemis, entre les mains de ceux qui cherchent leur vie, et leurs cadavres seront la pâture des oiseaux du ciel et des bêtes de la terre.
zan ba da su ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namun jeji.
21 Je livrerai aussi Sédécias, roi de Juda, avec ses princes, entre les mains de leurs ennemis et entre les mains de ceux qui cherchent leur vie, entre les mains de l'armée du roi de Babylone qui s'est éloigné de vous.
“Zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda da fadawansa ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, ga sojojin sarkin Babilon, waɗanda suke janye daga gare ku.
22 Voici, je vais donner ordre, dit l'Éternel, et je les ramènerai contre cette ville. Et ils combattront contre elle, et ils la prendront, et la brûleront; et je mettrai les villes de Juda en désolation, sans aucun habitant.
Zan yi umarni, in ji Ubangiji, zan kuma komo da su wannan birni. Za su kuwa yi yaƙi da ita, su ƙwace ta su kuma ƙone ta. Zan kuma mai da garuruwan Yahuda kufai don kada wani ya zauna a can.”