< Jérémie 30 >

1 La parole qui fut adressée à Jérémie de la part de l'Éternel, en ces termes:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Ainsi a parlé l'Éternel, le Dieu d'Israël: Écris dans un livre toutes les paroles que je t'ai dites.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ka rubuta a cikin littafi dukan maganganun da na yi maka.
3 Car voici, les jours viennent, dit l'Éternel, où je ramènerai les captifs de mon peuple d'Israël et de Juda, a dit l'Éternel; je les ramènerai dans le pays que j'ai donné à leurs pères, et ils le posséderont.
Kwanaki suna zuwa,’ in ji Ubangiji, ‘sa’ad da zan komo da mutanena Isra’ila da Yahuda daga bauta in kuma maido da su ga ƙasar da na ba wa kakanninsu mallaka,’ in ji Ubangiji.”
4 Et ce sont ici les paroles que l'Éternel a prononcées pour Israël et Juda;
Ga kalmomin Ubangiji da ya yi game da Isra’ila da Yahuda,
5 Car ainsi a dit l'Éternel: Nous entendons des cris d'effroi; c'est l'épouvante; et il n'y a point de paix!
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ana jin kukan tsoro, razana, ba salama ba.
6 Informez-vous, et voyez si un mâle enfante. Pourquoi vois-je tout homme les mains sur les reins, comme une femme en travail? Et pourquoi tous les visages sont-ils devenus livides?
Ku tambaya ku ji. Namiji zai iya haifi’ya’ya? To, me ya sa kuke ganin kowane mai ƙarfi da hannuwansa a kwankwaso kamar mace mai naƙuda, kowace fuska ta koma fari?
7 Hélas! c'est que cette journée est grande, et qu'il n'y en a point eu de semblable. C'est un temps de détresse pour Jacob! Pourtant il en sera délivré.
Kaito, gama wannan rana za tă zama mai girma! Babu kamar ta. Zai zama lokacin wahala wa Yaƙub, amma za a cece shi daga cikinta.
8 Et en ce jour-là, dit l'Éternel des armées, je briserai son joug de dessus ton cou, et je romprai tes liens; et les étrangers ne t'asserviront plus.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan karya karkiya daga wuyansu zan kuma cire musu kangi; baƙi ba za su ƙara bautar da su ba.
9 Ils serviront l'Éternel leur Dieu et David leur roi, que je leur susciterai.
A maimakon haka, za su bauta wa Ubangiji Allahnsu Dawuda sarkinsu kuwa, wanda na tayar musu.
10 Toi donc, mon serviteur Jacob, ne crains point, dit l'Éternel; ne t'épouvante pas, Israël! car voici, je te délivrerai de la terre lointaine, et ta postérité du pays de leur captivité. Alors Jacob reviendra, et il sera tranquille et à l'aise, et il n'y aura personne qui le trouble.
“‘Saboda haka kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila,’ in ji Ubangiji. ‘Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nesa, zuriyarka daga ƙasar zaman bautansu. Yaƙub zai sami salama da zaman lafiya, kuma ba wanda zai sa ya ji tsoro.
11 Car je suis avec toi, dit l'Éternel, pour te délivrer. Je détruirai entière-ment toutes les nations parmi lesquelles je t'ai dispersé; mais toi, je ne te détruirai point entièrement; je te châtierai avec mesure; cependant je ne te tiendrai pas pour innocent.
Ina tare da kai zan kuma cece ka,’ in ji Ubangiji. ‘Ko da yake na hallakar da dukan al’umma gaba ɗaya a inda na warwatsa ku, ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba. Zan hore ku amma da adalci kaɗai; ba zan ƙyale ku ku tafi gaba ɗaya ba hukunci ba.’
12 Car ainsi a dit l'Éternel: Ta blessure est incurable; ta plaie est sans espoir.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Mikinku marar warkewa ne, raunin da kuka ji ya sha ƙarfin warkarwa.
13 Nul ne prend ton parti, pour bander ta plaie; il n'y a pour toi nul remède, nul moyen de guérison.
Babu wanda zai yi roƙo saboda damuwarku, ba magani domin mikinku babu warkarwa dominku.
14 Tous ceux qui t'aiment t'ont oubliée; ils ne s'inquiètent plus de toi; car je t'ai frappée comme frappe un ennemi, comme châtie un homme cruel, à cause de la multitude de tes iniquités, parce que tes péchés se sont accrus.
Dukan abokanku sun manta da ku; ba su ƙara kulawa da ku. Na buge ku kamar yadda abokin gāba zai yi na kuma hukunta ku yadda mai mugunta zai yi, domin laifinku da girma yake zunubanku kuma da yawa suke.
15 Pourquoi cries-tu pour ta blessure? Ta douleur est incurable. C'est pour la grandeur de ton iniquité, parce que tes péchés se sont accrus, que je t'ai fait ces choses.
Me ya sa kuke kuka a kan mikinku, wahalarku da ba ta da magani? Domin laifinku da girma yake da kuma zunubanku masu yawa na yi muku waɗannan abubuwa.
16 Cependant tous ceux qui te dévorent seront dévorés, et tous tes oppresseurs, tous, s'en iront en captivité; ceux qui te dépouillent seront dépouillés, et je livrerai au pillage tous ceux qui te pillent.
“‘Amma duk wanda ya cinye ku za a cinye shi; dukan abokan gābanku za su tafi zaman bauta. Waɗanda suka washe ku su ma za a washe su; dukan waɗanda suka mai da ku ganima su ma zan mai da su ganima.
17 Mais je consoliderai tes plaies et je te guérirai, dit l'Éternel; car ils t'ont appelée la répudiée: c'est Sion, dont nul ne s'enquiert!
Amma zan mayar muku da lafiya in kuma warkar da mikinku,’ in ji Ubangiji, ‘domin ana ce da ku yasassu, Sihiyona wadda ba wanda ya kula da ita.’
18 Ainsi a dit l'Éternel: Voici je ramène les captifs des tentes de Jacob, et j'ai compassion de ses demeures; la ville sera rebâtie sur sa hauteur, et le palais habité selon l'usage.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Zan mayar da wadatar tentin Yaƙub in kuma ji tausayin wuraren zamansa; za a sāke gina birnin a kufansa, fadar kuwa za tă tsaya a wurin da ya dace da ita.
19 Et il en sortira des chants de louange et des cris de réjouissance. Je les multiplierai, et ils ne diminueront pas; je les honorerai, et ils ne seront pas avilis.
Daga gare su waƙoƙi za su fito na godiya da kuma sowa ta farin ciki. Zan riɓaɓɓanya su, ba za su kuwa ragu ba; zan kawo musu ɗaukaka, ba kuwa za a ƙasƙanta su ba.
20 Ses fils seront comme autrefois, son assemblée sera affermie devant moi, et je punirai tous ceux qui l'oppriment.
’Ya’yansu za su kasance kamar a kwanakin dā jama’arsu kuma za su kahu a gabana; zan hukunta duk wanda ya zalunce su.
21 Et son chef sera pris de lui, et son dominateur sera issu de son sein. Je le ferai approcher, et il viendra vers moi; car qui est celui qui exposerait son cœur à s'approcher de moi? dit l'Éternel.
Shugabansu zai zama ɗaya daga cikinsu; mai mulkinsu zai taso daga cikinsu. Zan kawo shi kusa zai kuma zo kusa da ni, gama wane ne zai miƙa kansa don yă yi kusa da ni?’ In ji Ubangiji.
22 Et vous serez mon peuple, et je serai votre Dieu.
‘Saboda haka za ku zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnku.’”
23 Voici, la tempête de l'Éternel, la fureur éclate, et l'orage prêt à fondre tombera sur la tête des méchants.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai fasu cikin hasala, iskar guguwa mai hurawa a kan kawunan mugaye.
24 L'ardeur de la colère de l'Éternel ne se détournera pas, jusqu'à ce qu'il ait exécuté et accompli les desseins de son cœur. Vous entendrez ceci dans les derniers jours.
Fushi mai zafi na Ubangiji ba zai kawu ba sai ya cika manufofin zuciyarsa gaba ɗaya. A kwanaki masu zuwa za ku gane wannan.

< Jérémie 30 >