< Jérémie 16 >
1 Puis la parole de l'Éternel me fut adressée en ces mots:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Tu ne prendras point de femme, et tu n'auras point dans ce lieu de fils ni de filles.
“Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
3 Car ainsi a dit l'Éternel, sur les fils et les filles qui naîtront en ce lieu, et sur leurs mères qui les auront enfantés, et sur leurs pères qui les auront engendrés dans ce pays:
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
4 Ils mourront de mort misérable; ils ne seront ni pleurés, ni ensevelis; mais ils seront comme du fumier sur la terre; ils seront consumés par l'épée et par la famine, et leurs cadavres serviront de pâture aux oiseaux des cieux et aux bêtes de la terre.
“Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
5 Car ainsi a dit l'Éternel: N'entre pas dans la maison de deuil, et ne va pas te lamenter ni t'affliger avec eux; car j'ai retiré de ce peuple ma paix, dit l'Éternel, ma grâce et mes compassions.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
6 Grands et petits mourront en ce pays; ils ne seront pas ensevelis: on ne les pleurera pas, on ne se fera point d'incisions, et l'on ne se rasera pas pour eux.
“Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
7 On ne rompra pas le pain dans le deuil, pour consoler quelqu'un au sujet d'un mort; on n'offrira pas la coupe de consolation, pour leur père ou pour leur mère.
Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
8 N'entre pas non plus dans la maison de festin, pour t'asseoir avec eux, pour manger ou pour boire.
“Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
9 Car ainsi a dit l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël: Voici, je ferai cesser en ce lieu, devant vos yeux et en vos jours, la voix de joie et la voix d'allégresse, la voix de l'époux et la voix de l'épouse.
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
10 Et quand tu auras annoncé à ce peuple toutes ces choses, et qu'ils te diront: “Pourquoi l'Éternel a-t-il prononcé tout ce grand mal contre nous? Quelle est donc notre iniquité, quel est le péché que nous avons commis contre l'Éternel notre Dieu?”
“Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
11 Tu leur diras: C'est parce que vos pères m'ont abandonné, dit l'Éternel, et sont allés après d'autres dieux et les ont servis, et se sont prosternés devant eux; parce qu'ils m'ont abandonné et n'ont pas gardé ma loi;
Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
12 Et que vous faites encore pis que vos pères. Car voici, chacun de vous marche suivant la dureté de son cœur méchant, pour ne point m'écouter.
Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
13 Aussi je vous transporterai de ce pays dans un pays que vous n'avez point connu, ni vous ni vos pères, et là vous servirez les autres dieux, jour et nuit, car je ne vous accorderai point de grâce.
Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
14 C'est pourquoi voici, les jours viennent, dit l'Éternel, où l'on ne dira plus: L'Éternel est vivant, lui qui a fait monter du pays d'Égypte les enfants d'Israël;
“Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
15 Mais on dira: L'Éternel est vivant, lui qui a fait monter les enfants d'Israël du pays du Nord, et de tous les pays où il les avait chassés; car je les ramènerai dans leur pays, que j'avais donné à leurs pères.
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
16 Voici, j'envoie de nombreux pêcheurs, dit l'Éternel, et ils les pêcheront; et après cela, j'enverrai de nombreux chasseurs, et ils les chasseront de toutes les montagnes, et de toutes les collines, et des fentes des rochers.
“Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
17 Car mes yeux sont sur toutes leurs voies; elles ne me sont point cachées, et leur iniquité n'est point couverte devant mes yeux.
Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
18 Et je leur rendrai d'abord le double de leur iniquité et de leur péché, parce qu'ils ont souillé ma terre par les cadavres de leurs infamies, et qu'ils ont rempli mon héritage de leurs abominations.
Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
19 Éternel! ma force, mon rempart, et mon refuge au jour de la détresse! les nations viendront à toi des bouts de la terre, et elles diront: Nos pères n'ont hérité que le mensonge, que des choses vaines, où il n'y a point de profit.
Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
20 L'homme se fera-t-il lui-même des dieux, qui ne sont pas des dieux?
Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
21 C'est pourquoi, voici, je leur ferai connaître cette fois, je leur ferai connaître ma force et ma puissance, et ils sauront que mon nom est l'Éternel.
“Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.