< Isaïe 58 >

1 Crie à plein gosier, ne te retiens pas; élève ta voix comme une trompette; déclare à mon peuple leur iniquité, à la maison de Jacob ses péchés!
“Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
2 Car, jour après jour, ils me cherchent et ils veulent connaître mes voies, comme une nation qui aurait pratiqué la justice et n'aurait pas abandonné la loi de son Dieu; ils me demandent des jugements justes, ils veulent s'approcher de Dieu:
Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
3 Pourquoi avons-nous jeûné, sans que tu y prisses garde, et affligé nos âmes, sans que tu le connusses? Voici, dans votre jour de jeûne, vous faites votre volonté et vous traitez durement tous vos mercenaires.
Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
4 Voici, vous jeûnez pour quereller et disputer, et pour frapper du poing méchamment; vous ne jeûnez pas comme le veut ce jour, pour que votre voix soit entendue en haut.
Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
5 Est-ce là le jeûne auquel je prends plaisir, un jour où l'homme afflige son âme? Est-ce de courber sa tête comme un jonc, de se coucher sur le sac et la cendre? Appelleras-tu cela un jeûne, un jour agréable à l'Éternel?
Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
6 N'est-ce pas plutôt ici le jeûne auquel je prends plaisir, qu'on dénoue les liens de la méchanceté, qu'on délie les courroies du joug, qu'on renvoie libres les opprimés, et que tout joug soit brisé?
“Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
7 N'est-ce pas que tu partages ton pain avec l'affamé; que tu fasses entrer dans ta maison les malheureux errants; que tu revêtes ceux que tu vois nus, et ne te détournes pas de ton semblable?
Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
8 Alors ta lumière poindra comme l'aurore, et ta guérison se montrera promptement; ta justice ira devant toi, et la gloire de l'Éternel sera ton arrière-garde.
Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
9 Alors tu appelleras, et l'Éternel répondra; tu crieras, et il dira: Me voici! Si tu ôtes du milieu de toi l'oppression, le doigt levé insolemment, et les paroles criminelles;
Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
10 Si tu fais part de ta subsistance à l'affamé, et que tu rassasies l'âme affligée, ta lumière se lèvera dans l'obscurité, et tes ténèbres seront comme le midi.
in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
11 L'Éternel te conduira continuellement; il te rassasiera dans les lieux arides; il donnera la vigueur à tes os, et tu seras comme un jardin arrosé, comme une source dont les eaux ne trompent jamais.
Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
12 Les tiens rebâtiront les antiques ruines, tu relèveras les fondations des anciens âges; on t'appellera le réparateur des brèches, le restaurateur des chemins, qui rend le pays habitable.
Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
13 Si tu retiens ton pied au jour du sabbat, pour ne pas faire ta volonté dans mon saint jour; si tu appelles le sabbat tes délices, et honorable ce qui est consacré à l'Éternel; si tu l'honores plutôt que de suivre tes voies, de faire ta volonté et de dire des paroles vaines:
“In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
14 Alors tu trouveras des délices en l'Éternel; je te ferai passer par-dessus les hauteurs du pays, et je te nourrirai de l'héritage de Jacob, ton père; car la bouche de l'Éternel a parlé.
sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.

< Isaïe 58 >