< Isaïe 50 >

1 Ainsi a dit l'Éternel: Où est la lettre de divorce de votre mère, par laquelle je l'ai renvoyée? Ou qui est celui de mes créanciers auquel je vous ai vendus? Voici, c'est pour vos iniquités que vous avez été vendus, c'est pour vos rébellions que votre mère a été renvoyée.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ina takardar shaida na saki mahaifiyarka daga aure wadda na kora? Ko kuwa ga wanda mutumin da nake bin bashi ne na sayar da kai? Saboda zunubanka aka sayar da kai; saboda laifofinka ne ya sa aka kori mahaifiyarka.
2 Pourquoi n'ai-je trouvé personne, quand je suis venu? Pourquoi nul n'a-t-il répondu, quand j'ai appelé? Ma main est-elle devenue trop courte pour délivrer, ou n'y a-t-il plus de force en moi pour sauver? Voici, je fais tarir la mer quand je la menace; je change les fleuves en désert; leurs poissons se corrompent faute d'eau, et ils meurent de soif.
Sa’ad da na zo, me ya sa babu kowa? Sa’ad da na yi kira, me ya sa babu wani da ya amsa? Hannuna ya kāsa ne sosai don fansarka? Na rasa ƙarfin kuɓutar da kai ne? Ta wurin tsawatawa kawai na busar da teku, na mai da koguna hamada; kifayensu duk sun ruɓe saboda rashin ruwa suka kuma mutu saboda ƙishi.
3 Je revêts les cieux de ténèbres, et j'y mets un manteau de deuil pour couverture.
Na suturar da sararin sama da duhu na kuma mai da tsummoki abin rufuwarsa.”
4 Le Seigneur, l'Éternel m'a donné une langue exercée, pour soutenir par la parole celui qui est abattu; il éveille, chaque matin, il éveille mon oreille pour écouter, comme écoutent les disciples.
Ubangiji Mai Iko Duka ya ba ni harshen umarni, don in san maganar da za tă ƙarfafa gajiyayye. Ya farkar da ni da safe, ya farkar da kunnena don in saurara kamar wanda ake koya masa.
5 Le Seigneur, l'Éternel m'a ouvert l'oreille, et je n'ai point résisté, je ne me suis point retiré en arrière.
Ubangiji Mai Iko Duka ya buɗe kunnuwana, kuma ban yi tayarwa ba; ban ja da baya ba.
6 J'ai présenté mon dos à ceux qui me frappaient, mes joues à ceux qui m'arrachaient la barbe; je n'ai pas dérobé mon visage aux outrages ni aux crachats.
Na ba da bayana ga masu dūkana, kumatuna ga masu jan gemuna; ban ɓoye fuskata daga masu ba’a da masu tofa mini miyau ba.
7 Mais le Seigneur, l'Éternel est mon aide; aussi je n'ai point eu de honte; aussi j'ai rendu mon visage semblable à un caillou; je sais que je ne serai pas confondu.
Gama Ubangiji Mai Iko Duka zai taimake ni, ba zan sha kunya ba. Saboda haka na kafa fuskata kamar dutsen ƙanƙara, na kuma sani ba zan sha kunya ba.
8 Celui qui me justifie est proche: qui plaidera contre moi? Comparais-sons ensemble! Qui est ma partie adverse? Qu'il s'approche de moi!
Gama shi da zai tabbatar da ni, marar laifi ne yana kusa. Wane ne zai kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari’a tare! Wane ne mai zargina? Bari yă kalubalance ni!
9 Voici, le Seigneur, l'Éternel est mon aide: qui me condamnera? Voici, ils s'useront tous comme un vêtement, la teigne les dévorera.
Ubangiji Mai Iko Duka ne zai taimake ni. Wane ne zai iya tabbatar da ni mai laifi? Duk za su koɗe kamar riga; asu za su cinye su.
10 Qui d'entre vous craint l'Éternel, qui écoute la voix de son serviteur? Que celui qui marche dans les ténèbres, et qui n'a point de lumière, se confie au nom de l'Éternel, et qu'il s'appuie sur son Dieu.
Wane ne a cikinku yake tsoron Ubangiji yana kuma yin biyayya ga maganar bawansa? Bari wanda yake tafiya cikin duhu, wanda ba shi da haske, ya dogara a sunan Ubangiji ya kuma dogara ga Allahnsa.
11 Voici, vous tous qui allumez un feu et qui vous armez de flambeaux, tombez dans les flammes de votre feu et des flambeaux que vous avez allumés! C'est de ma main que vous vient cela: vous serez gisants dans les tourments!
Amma yanzu fa, dukanku waɗanda kuke ƙuna wuta kuna kuma tanada wa kanku fitilu masu ci, ku je ku yi tafiya a cikin hasken wutarku da na fitilun da kuka ƙuna. Abin da za ku karɓa ke nan daga hannuna. Za ku kwanta a cikin azaba.

< Isaïe 50 >