< Genèse 10 >

1 Voici les descendants des fils de Noé: Sem, Cham et Japhet, auxquels naquirent des enfants après le déluge.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Les fils de Japhet sont Gomer, Magog, Madaï, Javan, Tubal, Méshec, et Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 Et les fils de Gomer, Ashkénas, Riphath, et Togarma.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Et les fils de Javan, Elisha et Tarsis, Kittim et Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 Par eux furent peuplées les îles des nations, dans leurs terres, chacun selon sa langue, selon leurs familles, selon leurs nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Et les fils de Cham, sont Cush, Mitsraïm, Put et Canaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 Et les fils de Cush, Seba, Havila, Sabta, Raema et Sabteca. Et les fils de Raema, Sheba et Dedan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Et Cush engendra Nimrod, qui commença à être puissant sur la terre.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 Il fut un puissant chasseur devant l'Éternel. C'est pour cela qu'on dit: Comme Nimrod, puissant chasseur devant l'Éternel.
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 Et le commencement de son royaume fut Babel, Érec, Accad et Calné, dans le pays de Shinear.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 De ce pays-là il sortit en Assyrie, et il bâtit Ninive, Rehoboth-Ir, Calach,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 Et Résen, entre Ninive et Calach; c'est la grande ville.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Et Mitsraïm engendra les Ludim, les Anamim, les Lehabim, les Naphtuhim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 Les Pathrusim, les Casluhim (d'où sont sortis les Philistins) et les Caphtorim.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Et Canaan engendra Sidon, son premier-né, et Heth;
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 Les Jébusiens, les Amoréens, les Guirgasiens;
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 Les Héviens, les Arkiens, les Siniens;
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 Les Arvadiens, les Tsemariens, les Hamathiens. Ensuite les familles des Cananéens se dispersèrent.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 Et la limite des Cananéens fut depuis Sidon, en venant vers Guérar, jusqu'à Gaza, en venant vers Sodome, Gomorrhe, Adma, et Tseboïm, jusqu'à Lésha.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 Ce sont là les fils de Cham, selon leurs familles, selon leurs langues, dans leurs terres, dans leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Il naquit aussi des fils à Sem, père de tous les fils d'Héber, et frère aîné de Japhet.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Les fils de Sem sont Élam, Assur, Arpacshad, Lud et Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 Et les fils d'Aram, Uts, Hul, Guéther et Mash.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Et Arpacshad engendra Shélach, et Shélach engendra Héber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 Et à Héber il naquit deux fils: le nom de l'un est Péleg (partage), car en son temps la terre fut partagée; et le nom de son frère, Jockthan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Et Jockthan engendra Almodad, Sheleph, Hatsarmaveth, et Jérach;
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 Hadoram, Uzal, Dikla,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 Obal, Abimaël, Sheba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 Ophir, Havila, et Jobab. Tous ceux-là sont fils de Jockthan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 Et leur demeure était depuis Mésha, en venant vers Sephar, vers la montagne d'Orient.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 Ce sont là les fils de Sem, selon leurs familles, selon leurs langues, selon leurs terres, selon leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 Telles sont les familles des fils de Noé, selon leurs générations, dans leurs nations; et c'est d'eux que sont sorties les nations de la terre après le déluge.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Genèse 10 >