< Ézéchiel 24 >
1 La neuvième année, le dixième jour du dixième mois, la parole de l'Éternel me fut adressée, en ces termes:
A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, note-toi la date de ce jour, de ce jour même; aujourd'hui le roi de Babylone s'approche de Jérusalem.
“Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
3 Propose une parabole à la maison rebelle, et dis-leur: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Mets en place la chaudière, place-la, et verses-y de l'eau.
Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
4 Mets-y ensemble des morceaux, tous les bons morceaux, les cuisses et les épaules, et remplis-la des meilleurs os.
Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
5 Choisis la meilleure pièce du troupeau, et entasse du bois sous la chaudière; fais bouillir à gros bouillons, afin que les os qui sont dedans cuisent aussi.
ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
6 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Malheur à la ville sanguinaire, chaudière rouillée, et dont la rouille ne s'en va pas! Vide-la pièce par pièce, sans recourir au sort.
“‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
7 Car le sang qu'elle a répandu est au milieu d'elle; elle l'a mis sur le roc nu, elle ne l'a pas versé sur la terre pour le couvrir de poussière.
“‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
8 Afin de faire monter ma fureur et pour me venger, je l'ai laissée répandre son sang sur le roc nu, afin qu'il ne fût pas couvert.
Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
9 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Malheur à la ville sanguinaire! moi aussi je vais dresser un grand bûcher.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
10 Entasse du bois, allume le feu, cuis la chair entièrement, fais fondre la graisse et que les os se consument.
Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
11 Puis place la chaudière vide sur les charbons ardents, afin qu'elle s'échauffe, que son airain devienne brûlant, que sa souillure se fonde au-dedans, et que sa rouille soit consumée.
Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
12 Elle lasse tous mes efforts, et la rouille dont elle est remplie ne s'en va point; au feu donc la rouille!
Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
13 Ta souillure est criminelle, puisque j'ai voulu te purifier et que tu n'es point devenue pure; tu ne seras plus nettoyée de ta souillure jusqu'à ce que j'aie assouvi contre toi ma fureur.
“‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
14 Moi, l'Éternel, j'ai parlé; cela arrivera, et je le ferai; je ne reculerai point, et je n'aurai ni pitié, ni repentir. On te jugera selon ta conduite et selon tes actions, dit le Seigneur, l'Éternel!
“‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 La parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 Fils de l'homme, voici, par une plaie soudaine, j'enlève ce qui fait les délices de tes yeux; mais tu ne mèneras point deuil, tu ne pleureras point, et tu ne laisseras pas couler tes larmes.
“Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
17 Soupire en silence, mais ne prends pas le deuil des morts; attache ta coiffure sur toi, mets ta chaussure à tes pieds, ne te voile pas la barbe et ne mange pas le pain des autres.
Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
18 Le matin je parlai donc au peuple; et le soir ma femme mourut; et le lendemain matin je fis comme il m'avait été commandé.
Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
19 Alors le peuple me dit: Ne nous expliqueras-tu pas ce que signifie pour nous ce que tu fais?
Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
20 Et je répondis: La parole de l'Éternel m'a été adressée, en ces termes:
Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
21 Dis à la maison d'Israël: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Voici, je vais profaner mon sanctuaire, l'orgueil de votre puissance, les délices de vos yeux, l'affection de votre âme, et vos fils et vos filles que vous avez laissés tomberont par l'épée.
faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
22 Vous ferez alors comme j'ai fait; vous ne vous voilerez point la barbe, et vous ne mangerez pas le pain des autres;
Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
23 Vos coiffures seront sur vos têtes, et votre chaussure à vos pieds; vous ne mènerez point deuil, et ne pleurerez pas; mais vous serez frappés de langueur à cause de vos iniquités, et vous gémirez les uns avec les autres.
Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
24 Ézéchiel sera pour vous un signe, et tout ce qu'il a fait vous le ferez aussi. Quand cela arrivera, vous saurez que je suis le Seigneur, l'Éternel.
Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
25 Et toi, fils de l'homme, le jour où je leur ôterai leur force, leur joie, leur gloire, les délices de leurs yeux, l'objet de leur amour, leurs fils et leurs filles,
“Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
26 Ce jour-là un fuyard viendra vers toi pour l'annoncer à tes oreilles.
a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
27 En ce jour-là, ta bouche s'ouvrira en même temps que celle du fuyard; tu parleras, tu ne seras plus muet; et tu seras pour eux un signe, et ils sauront que je suis l'Éternel.
A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”