< Ézéchiel 16 >
1 La parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, fais connaître à Jérusalem ses abominations.
“Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta masu banƙyama
3 Dis: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel, à Jérusalem: Par ton origine et ta naissance tu es du pays de Canaan; ton père est un Amoréen, ta mère une Héthienne.
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wa Urushalima, Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan’ana ne; mahaifinki mutumin Amoriyawa ne, mahaifiyarki kuma mutuniyar Hitti ce.
4 A ta naissance, au jour où tu naquis, ton nombril ne fut point coupé, tu ne fus point lavée dans l'eau pour être nettoyée, tu ne fus pas purifiée avec du sel, ni enveloppée de langes.
A ranar da aka haife ki ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka don a tsabtacce ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba ko a naɗe ki cikin tsummoki.
5 Aucun œil n'eut pitié de toi, pour te faire aucune de ces choses par compassion pour toi; mais tu fus jetée sur la surface d'un champ, par mépris pour ta vie, au jour de ta naissance.
Ba wanda ya dube ki da tausayi ko ya nuna miki isashen jinƙai don yă yi miki ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. A maimako, sai aka jefar da ke a fili, gama a ranar da aka haife ki an ji ƙyamarki.
6 Or je passai près de toi, je te vis gisant dans ton sang, près d'être foulée aux pieds, et je te dis: Vis dans ton sang! je te dis: Vis dans ton sang!
“‘Sa’an nan na wuce na ga kina birgima cikin jininki, yayinda kike kwance can cikin jininki sai na ce miki, “Ki rayu!”
7 Je t'ai multipliée par myriades, comme l'herbe des champs, tu pris de l'accroissement, tu grandis et tu devins d'une beauté parfaite. Tes seins se formèrent, tu devins nubile, mais tu étais nue, et entièrement nue.
Na sa kin yi girma kamar tsiro a fili. Kin yi girma kika kuma yi tsayi kika zama mafiya kyau na kayan ado. Nononki suka fito, gashinki kuwa suka yi girma, duk da haka tsirara kike tik.
8 Et je passai près de toi et te regardai; voici, ton âge était l'âge où l'on aime, et j'étendis sur toi le pan de mon vêtement, je couvris ta nudité; je te fis serment, je fis alliance avec toi, dit le Seigneur, l'Éternel, et tu m'appartins.
“‘Daga baya na wuce, da na dube ki sai na ga cewa kin yi girma sosai har kin kai a ƙaunace ki, na yafa gefen tufafina a kanki na kuma rufe tsiraincinki. Na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Je te lavai dans l'eau, et en t'y plongeant, j'ôtai le sang de dessus toi, et je t'oignis d'huile.
“‘Na yi miki wanka na wanke miki jini daga gare ki na kuma shafa miki mai.
10 Je te revêtis de broderies, je te mis une chaussure de couleur d'hyacinthe; je te ceignis de fin lin et te couvris de soie.
Na rufe ki da rigar da aka yi wa ado na kuma sa miki takalman fata. Na sa miki riga ta lilin mai kyau na kuma rufe ki da riguna masu tsada.
11 Je te parai d'ornements; je mis des bracelets à tes mains, et un collier à ton cou,
Na yi miki ado da kayan ado masu daraja, na sa miki mundaye a hannuwanki da abin wuya a wuyanki,
12 Un anneau à ton nez, des boucles à tes oreilles, une couronne magnifique sur ta tête.
na kuma sa miki zobe a hancinki, abin kunne a kunnuwanki da rawani mai kyau a kanki.
13 Ainsi tu fus parée d'or et d'argent; ton vêtement était de fin lin, de soie, de broderies; la fleur de farine, le miel et l'huile faisaient ta nourriture; tu devins extrêmement belle, et tu parvins à une royale dignité.
Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa; tufafinki kuwa na lilin mai kyau da riguna masu tsada waɗanda aka yi musu ado. Abincinki na gari mai laushi ne, zuma da man zaitun. Kika zama kyakkyawa har kika kuma zama sarauniya.
14 Ta renommée se répandit parmi les nations à cause de ta beauté, car elle était parfaite, grâce à la magnificence dont je t'avais ornée, dit le Seigneur, l'Éternel.
Sunanki ya yaɗu a cikin al’ummai saboda kyanki, domin darajar da na ba ki ya sa kyanki ya zama cikakke, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Mais tu t'es confiée en ta beauté, tu t'es prostituée à la faveur de ta renommée, et tu as prodigué tes prostitutions à tout passant, en te livrant à lui.
“‘Amma kika dogara ga kyanki kika kuma yi amfani da sunan da kika yi don ki zama karuwa. Kin yi ta jibga alherai a kan kowa da ya wuce, sai kyanki ya zama naki.
16 Tu as pris de tes vêtements; tu t'es fait des hauts lieux garnis d'étoffes de toute couleur, et tu t'y es prostituée, - chose qui n'était point arrivée, et qui n'arrivera plus.
Kin ɗauki waɗansu tufafinki don ki yi wa kanki masujadai masu ado, inda kike karuwancinki. Irin waɗannan abubuwa bai kamata su faru ba, bai kuma kamata su taɓa faruwa ba.
17 Tu as aussi pris les magnifiques parures, faites de mon or et de mon argent, que je t'avais données; tu en as fait des figures d'hommes, auxquels tu t'es prostituée.
Kika kuma ɗauki kayan ado masu kyau da na ba ki, kayan adon da aka yi da zinariya da azurfa, kika yi wa kanki gumakan maza kika kuma yi ta yin karuwanci da su.
18 Tu as pris tes vêtements brodés pour les en couvrir, et tu leur as offert mon huile et mes parfums.
Kika ɗauki rigunanki masu ado don ki sa a kansu, kika kuma miƙa maina da turarena a gabansu.
19 Et mon pain que je t'avais donné, la fleur de farine, l'huile et le miel dont je te nourrissais, tu as mis ces choses devant elles comme une offrande d'agréable odeur. Voilà ce qui en est, dit le Seigneur, l'Éternel.
Haka ma abincin da na tanada miki, lallausan gari, man zaitun, da zuman da na ba ki ki ci, kin miƙa su kamar turare mai ƙanshi a gabansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
20 Tu as pris tes fils et tes filles, que tu m'avais enfantés, et tu les leur as sacrifiés pour être dévorés. Était-ce trop peu que tes prostitutions?
“‘Kika kuma kwashe’ya’yanki maza da mata waɗanda kin haifa mini kika miƙa su kamar abinci ga gumakanki. Karuwancinki bai isa ba ne?
21 Tu as immolé mes fils, tu les as livrés, en les faisant passer par le feu en leur honneur.
Kin kashe’ya’yana kika kuma miƙa su ga gumaka.
22 Et au milieu de toutes tes abominations et de tes adultères, tu ne t'es point souvenue du temps de ta jeunesse, alors que tu étais nue et découverte, gisante dans ton sang, près d'être foulée aux pieds.
Cikin dukan ayyukan banƙyamarki da karuwancinki ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba, sa’ad da kike tsirara tik, kina birgima cikin jininki.
23 Et après toutes tes méchantes actions, - malheur, malheur à toi! dit le Seigneur, l'Éternel, -
“‘Kaito! Kaitonki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Bugu da ƙari a kan dukan waɗansu muguntarki,
24 Tu t'es bâti des maisons de débauche, tu t'es fait des hauts lieux sur toutes les places.
kin gina wa kanki ɗakunan sama da gidajen tsafi a kowane dandali.
25 A l'entrée de chaque rue tu as bâti ton haut lieu, et tu as déshonoré ta beauté; car tu t'es livrée à tout passant et tu as multiplié tes adultères.
A kowane titi kin gina ɗakin tsafi kika kuma wulaƙanta kyanki, kina miƙa jikinki da ƙarin fasikanci ga duk mai wucewa.
26 Tu t'es prostituée aux enfants de l'Égypte, tes voisins aux corps vigoureux, et pour m'irriter tu as multiplié tes adultères.
Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi, kika tsokane ni har na yi fushi da ƙarin fasikancinki.
27 Et voici, j'ai étendu ma main contre toi, j'ai diminué la part qui t'était assignée, et t'ai livrée à la discrétion de tes ennemis, les filles des Philistins, qui ont rougi de ta conduite criminelle.
Saboda haka na miƙa hannuna gāba da ke na kuma rage iyakarki; na ba da ke ga abokan gābanki masu haɗama,’yan matan Filistiyawa, waɗanda suka sha mamaki saboda halinki na lalata.
28 Tu t'es prostituée aux enfants de l'Assyrie, parce que tu n'étais pas assouvie; et après avoir commis adultère avec eux, tu ne fus point encore assouvie;
Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa, domin ba kya ƙoshi; kai ko bayan wannan, ba ki ƙoshi ba.
29 Car tu as multiplié tes impudicités avec la terre de Canaan et jusqu'en Caldée; même alors tu n'en eus point assez.
Sai kika ƙara fasikancinki da ya haɗa da ƙasar cinikin Babilon, amma duk da haka ba ki ƙoshi ba.
30 Combien ton cœur est lâche, dit le Seigneur, l'Éternel, que tu aies fait toutes ces choses à la façon d'une insigne prostituée!
“‘Kina da rashin ƙarfi a zuci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da kika yi duk waɗannan abubuwa, kina yi kamar karuwar da aka watsa!
31 Quand tu bâtissais tes maisons de débauche à chaque bout de rue, quand tu faisais tes hauts lieux dans toutes les places, tu n'as pas même été comme la femme débauchée qui réclame un salaire;
Sa’ad da kika gina ɗakunan samanki a kowane gefen titi kika kuma gina ɗakunan tsafinki a kowane dandali, ba kamar karuwa kike ba, domin kin karɓi kuɗi.
32 Tu as été la femme adultère qui reçoit les étrangers à la place de son mari.
“‘Ke mazinaciyar mace! Kin gwammace baƙi a maimakon mijinki!
33 On paie un salaire à toutes les femmes débauchées, mais toi, tu as donné des présents à tous tes amants; tu leur as fait des largesses, afin que de toute part ils viennent vers toi, pour tes prostitutions.
Kowace karuwa kan karɓi kuɗi, amma kina ba da kyautai ga dukan kwartayenki, kina ba su cin hanci don su zo wurinki daga ko’ina don alherai marasa ƙa’ida.
34 Et tu as été le contraire des autres femmes dans tes impudicités, en ce qu'on ne te recherchait pas; tu donnais un salaire, tandis que l'on ne t'en donnait aucun; tu as été le contraire des autres.
Saboda haka cikin karuwancinki kin sha bamban da saura; babu wanda yake binki saboda alheranki. Ke dai dabam ce, gama kikan biya kuma ba mai biyanki.
35 C'est pourquoi, ô prostituée, écoute la parole de l'Éternel!
“‘Saboda haka, ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji!
36 Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Parce que tes trésors ont été prodigués, et que ta nudité s'est découverte dans tes prostitutions, devant tes amants et toutes tes abominables idoles; à cause du sang de tes enfants, que tu leur as livrés,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kin zubar da dukiyarki kika bayyana tsiraicinki cikin fasikancinki da kwartayenki, kuma saboda dukan gumakan banƙyamarki, kuma saboda kin ba su jinin’ya’yansu,
37 Voici, je rassemblerai tous tes amants, avec lesquels tu te plaisais, tous ceux que tu as aimés, tous ceux que tu as haïs, je les rassemblerai de toute part contre toi; je leur découvrirai ta nudité, et ils la verront tout entière.
saboda haka zan tattara dukan kwartayenki, waɗanda kike jin daɗinsu, waɗanda kike ƙauna da waɗanda kike ƙi. Zan tattara su gāba da ke daga dukan kewaye zan kuma tuɓe ki a gabansu, za su kuwa ga dukan tsiraicinki.
38 Et je te jugerai comme on juge les femmes adultères et celles qui répandent le sang; je t'abandonnerai à la sanguinaire vengeance de la fureur et de la jalousie.
Zan hukunta ki da hukuncin matan da suke zina da kuma waɗanda suke zub da jini; zan kawo hakkin jini na fushina da kuma fushin kishina.
39 Je te livrerai entre leurs mains; ils abattront tes maisons de débauche et démoliront tes hauts lieux; ils te dépouilleront de tes vêtements; ils enlèveront tes magnifiques parures et te laisseront nue, entièrement nue.
Sa’an nan zan miƙa ki ga kwartayenki, za su kuwa rurrushe ɗakunan samanki su kuma farfashe ɗakunan tsafinki. Za su tuɓe miki tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau su bar ki tsirara tik.
40 Ils feront monter contre toi une foule de gens qui t'assommeront de pierres, et qui te mettront en pièces avec leurs épées.
Za su kawo taron jama’a a kanki, waɗanda za su jajjefe ki da dutse su sassare ki gunduwa-gunduwa da takubansu.
41 Ils brûleront tes maisons par le feu, et feront justice de toi, en présence d'un grand nombre de femmes; ainsi je mettrai fin à tes prostitutions, et tu ne donneras plus de salaire.
Za su ƙone gidajenki su kuma hukunta ki a idon mata masu yawa. Zan kawo ƙarshen karuwancinki, ba za ki kuma ƙara biyan kwartayenki ba.
42 Et j'assouvirai ma fureur contre toi, et ma jalousie se détournera de toi; alors je serai en repos et n'aurai plus à m'irriter.
Sa’an nan fushina a kanki zai huce fushin kishina kuma ya kwanta; zan huce ba kuwa zan ƙara yin fushi ba.
43 Parce que tu ne t'es point souvenue du temps de ta jeunesse, que tu m'as provoqué par toutes ces choses, voici, je ferai retomber ta conduite sur ta tête, dit le Seigneur, l'Éternel, et tu ne commettras plus le crime avec toutes tes abominations.
“‘Domin ba ki tuna da kwanakin ƙuruciyarki ba amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, tabbatacce zan sāka miki alhakin ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ba kin ƙara lalata ga dukan waɗansu ayyuka masu banƙyamarki ba?
44 Voici, tout homme qui use de proverbes, en fera un sur ton compte, et dira: “Telle mère, telle fille! “
“‘Duk mai yin amfani da karin magana zai faɗi wannan karin magana a kanki cewa, “Kamar yadda mahaifiya take haka’yar take.”
45 Tu es la fille de ta mère, qui eut en aversion son mari et ses enfants; tu es la sœur de tes sœurs, qui ont eu en aversion leurs maris et leurs enfants; votre mère était Héthienne et votre père Amoréen.
Ke’yar mahaifiyarki ce da gaske, wadda ta ƙi mijinta da’ya’yanta; ke kuma’yar’uwar’yar’uwanki mata ce da gaske, waɗanda suka ƙi mazansu da’ya’yansu. Mahaifiyarki mutuniyar Hitti ce, mahaifinki kuma mutumin Amoriyawa ne.
46 Ta sœur aînée, avec ses filles, qui habite à ta gauche, c'est Samarie; ta sœur cadette qui demeure à ta droite, c'est Sodome et ses filles.
Babbar’yar’uwarki mutuniyar Samariya ce, wadda take zaune da’ya’yanta mata wajen arewa da ke; ƙanuwarki ita ce Sodom wadda take zaune kudu da ke tare da’ya’yanta mata.
47 Tu n'as pas seulement marché dans leurs voies et pratiqué les mêmes abominations; c'était trop peu; mais tu t'es corrompue plus qu'elles dans toute ta conduite.
Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.
48 Je suis vivant! dit le Seigneur, l'Éternel; Sodome, ta sœur elle-même, avec ses filles, n'a point fait ce que tu as fait, toi, avec tes filles.
Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka,’yar’uwarki Sodom da’ya’yanta mata ba su yi abin da’ya’yanki mata suka yi ba.
49 Voici quelle a été l'iniquité de Sodome, ta sœur: l'orgueil, l'abondance et une molle oisiveté; voilà ce qu'elle avait, elle et ses filles; mais elle ne soutenait pas la main de l'affligé et du pauvre.
“‘To, fa, ga zunubin’yar’uwarki Sodom. Ita da’ya’yanta mata sun yi girman kai, sun ƙoshi fiye da kima kuma ba su kula da wani abu ba; ba su taimaki matalauta da kuma masu bukata ba.
50 Elles sont devenues hautaines et ont commis l'abomination devant moi; aussi les ai-je exterminées, dès que je l'ai vu.
Su masu girman kai ne kuma suka aikata abubuwa masu banƙyama a gabana. Saboda haka na kau da su kamar yadda ka gani.
51 Et Samarie n'a pas commis la moitié autant de péchés que toi; tu as multiplié tes abominations plus qu'elle, et par toutes les abominations que tu as commises tu as justifié tes sœurs.
Samariya ba tă aikata ko rabin zunubanki ba. Kin aikata abubuwa masu banƙyama fiye da su, suka kuma sa’yan’uwanki mata suka zama kamar masu adalci ta wurin dukan waɗannan abubuwa da kika aikata.
52 Porte donc, toi aussi, l'opprobre que tu as infligé à tes sœurs! A cause de tes péchés que tu as rendus plus abominables que les leurs, elles se trouvent être plus justes que toi. Sois donc, toi aussi, couverte de confusion, et porte ton opprobre, puisque tu as justifié tes sœurs.
Ki sha kunyarki, gama kin yi rangwame wa’yan’uwanki mata. Saboda zunubanki sun yi muni fiye da nasu, sai suka zama kamar sun fi ki adalci. Saboda haka, ki sha kunya ki kuma sha ƙasƙancinki, gama kin sa’yan’uwanki mata suka zama kamar su masu adalci ne.
53 Je ramènerai leurs captifs, les captifs de Sodome et de ses filles, les captifs de Samarie et de ses filles, ainsi que tes propres captifs au milieu des leurs,
“‘Amma fa, zan komo da nasarar Sodom da’ya’yanta mata da ta Samariya da’ya’yanta mata, nasararki kuma tare da su,
54 Afin que tu portes ton opprobre, que tu sois confuse à cause de tout ce que tu as fait, en étant pour elles un sujet de consolation.
domin ki sha ƙasƙancinki ki kuma sha kunyar dukan abin da kika aikata ta wurin ta’azantar da su.
55 Et tes sœurs, Sodome et ses filles, reviendront à leur premier état; Samarie et ses filles reviendront à leur premier état; et toi et tes filles vous reviendrez à votre premier état.
’Yan’uwanki kuwa, Sodom da’ya’yanta mata da Samariya tare da’ya’yanta mata, za su koma kamar yadda suke a dā; ke kuma da’ya’yanki mata za ku koma kamar yadda kike a dā.
56 Cependant, dans le temps de ton orgueil,
Ba za ki ma iya ambaci’yar’uwarki Sodom a ranar fariyarki ba,
57 Avant que ta méchanceté fût découverte, lorsque tu recevais les outrages des filles de Syrie et de tous ses alentours, des filles des Philistins qui t'insultaient de toute part, ne discourais-tu pas sur Sodome ta sœur?
kafin a tone muguntarki. Ko da ma haka, yanzu’ya’yan Arameyawa mata da dukan maƙwabtanta da kuma’ya’yan Filistiyawa mata suna miki dariyar, dukan waɗanda suke kewaye da ke da suka rena ki.
58 Tu portes sur toi le fardeau de tes crimes et de tes abominations! dit l'Éternel.
Za ki ɗauki hakkin lalatarki da kuma ayyukanki masu banƙyama, in ji Ubangiji.
59 Car ainsi a dit l'Éternel: Je te ferai comme tu as fait, toi qui as méprisé le serment, en rompant l'alliance.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta kamar yadda ya dace da ke, domin kin ƙyale rantsuwana ta wurin karya alkawari.
60 Toutefois je me souviendrai de l'alliance que j'ai faite avec toi, dans les jours de ta jeunesse, et j'établirai en ta faveur une alliance éternelle.
Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin ƙuruciyarki, zan kuma kafa madawwamin alkawari da ke.
61 Alors tu te souviendras de ta conduite, et tu en seras confuse, quand tu recevras tes sœurs, tant les aînées que les cadettes, et que je te les donnerai pour filles, mais non en vertu de ton alliance.
Sa’an nan za ki tuna da hanyoyinki ki kuma ji kunya sa’ad da kika karɓi’yan’uwanki mata, waɗanda suka girme ki da kuma waɗanda kika girme su. Zan ba da su kamar’ya’ya mata gare ki, amma ba bisa alkawarina da ke ba.
62 Car j'établirai mon alliance avec toi, et tu sauras que je suis l'Éternel,
Ta haka zan kafa alkawarina da ke, za ki kuma san cewa ni ne Ubangiji.
63 Afin que tu te souviennes, que tu sois confuse, et qu'à cause de ta confusion tu n'ouvres plus la bouche, quand je t'aurai pardonné tout ce que tu as fait, dit le Seigneur, l'Éternel.
Sa’an nan, sa’ad da na yi kafara saboda ke domin dukan abin da kika aikata, za ki tuna ki kuma ji kunya har ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”