< Ézéchiel 15 >
1 La parole de l'Éternel me fut adressée en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Fils de l'homme, le bois de la vigne vaut-il plus que tout autre bois, le sarment qui est parmi les arbres de la forêt
“Ɗan mutum, da me itacen kuringa ya fi reshen waɗansu itatuwa kyau a cikin kurmi?
3 Prend-on de ce bois pour faire quelque ouvrage; en tire-t-on une cheville pour y suspendre un objet quelconque?
An taɓa ɗaukan itacensa an yi wani abu mai amfani? Akan yi maratayi da ita da za a rataya wani abu a kai?
4 Voici, on le jette au feu pour le consumer, et quand le feu en a dévoré les deux bouts, et que le milieu brûle, est-il propre à quelque ouvrage?
Bayan kuma a jefa ta cikin wuta, wuta kuma ta cinye kowane gefe ta kuma babbaka tsakiyarta, tana da amfani don yin wani abu kuma?
5 Voici, quand il était entier, on n'en faisait aucun ouvrage; combien moins encore quand le feu l'a dévoré et qu'il est brûlé, en pourra-t-on faire quelque chose?
In ba ta da amfanin wani abu sa’ad da take cikakkiya, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita?
6 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: De même que parmi les arbres d'une forêt, c'est le bois de la vigne que je livre au feu pour être dévoré, de même j'y livrerai les habitants de Jérusalem.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kamar yadda na ba da itacen kuringa a cikin itatuwan kurmi ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama.
7 Je tournerai ma face contre eux; s'ils sortent d'un feu, un autre feu les consumera, et vous saurez que je suis l'Éternel, quand je tournerai ma face contre eux.
Zan yi gāba da su. Ko da yake sun fito daga wuta, wuta za tă cinye su. Kuma sa’ad da na yi gāba da su, za ku san cewa ni ne Ubangiji.
8 Je ferai du pays un désert, parce qu'ils ont été infidèles, dit le Seigneur, l'Éternel!
Zan mai da ƙasar kufai domin sun yi rashin aminci, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”