< 2 Samuel 11 >

1 L'an d'après, au temps où les rois se mettaient en campagne, David envoya Joab, et avec lui ses serviteurs et tout Israël; et ils ravagèrent le pays des enfants d'Ammon et assiégèrent Rabba. Mais David demeura à Jérusalem.
Da bazara, a lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, sai Dawuda ya aiki Yowab tare da mutanen sarki, da dukan Isra’ila. Suka je suka hallaka Ammonawa, suka kuma yi wa Rabba kwanton ɓauna. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima.
2 Et il arriva, sur le soir, que David se leva de dessus son lit; et comme il se promenait sur la plate-forme du palais royal, il vit de cette plate-forme une femme qui se baignait, et cette femme était fort belle à voir.
Wata rana da yamma, Dawuda ya tashi daga gadonsa, ya zaga kewaye a rufin fadansa. Daga rufin ya ga wata mace tana wanka. Matar kyakkyawa ce ƙwarai.
3 Et David envoya demander qui était cette femme, et on lui dit: N'est-ce pas Bath-Shéba, fille d'Éliam, femme d'Urie, le Héthien?
Sai Dawuda ya aiki wani yă bincika ko wace ce ita, sai mutumin ya dawo ya ce, “Wannan ba Batsheba ba ce,’yar Eliyam matar Uriya, mutumin Hitti?”
4 Et David envoya des messagers, et l'enleva. Elle vint vers lui, et il coucha avec elle; or elle était nettoyée de sa souillure; puis elle s'en retourna dans sa maison.
Sa’an nan Dawuda ya aiki manzanni su kawo masa ita. Ta zo wurinsa shi kuma ya kwana da ita (A lokacin kuwa ta gama tsarkake kanta ke nan daga jinin haila.) Sa’an nan ta tafi gida.
5 Or cette femme conçut, et elle envoya l'annoncer à David, en lui disant: Je suis enceinte.
Matar ta yi ciki, ta kuwa aika wa Dawuda, tana cewa, “Ina da ciki.”
6 Alors David fit dire à Joab: Envoie-moi Urie, le Héthien. Joab envoya donc Urie vers David.
Saboda haka Dawuda ya aika saƙo wa Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya mutumin Hitti.” Yowab kuwa ya aika da shi wajen Dawuda.
7 Et Urie vint à lui, et David l'interrogea sur l'état de Joab et du peuple, et sur l'état de la guerre.
Da Uriya ya zo wurinsa, sai Dawuda ya tambaye shi lafiyar Yowab da sojojin, da kuma yaya yaƙin yake tafiya.
8 Puis David dit à Urie: Descends dans ta maison et te lave les pieds. Urie sortit donc de la maison du roi, et il fut suivi d'un présent royal.
Sa’an nan Dawuda ya ce wa Uriya, “Gangara gidanka ka wanke ƙafafunka.” Saboda haka Uriya ya bar fadar, sarki kuma ya aika masa da kyauta.
9 Mais Urie dormit à la porte de la maison du roi, avec tous les serviteurs de son seigneur, et ne descendit point dans sa maison.
Amma Uriya ya kwanta a ƙofar fada tare da dukan bayin maigidansa, bai kuwa tafi gidansa ba.
10 Et on le rapporta à David, et on lui dit: Urie n'est pas descendu dans sa maison. Et David dit à Urie: Ne viens-tu pas de voyage? Pourquoi n'es-tu pas descendu dans ta maison?
Da aka gaya wa Dawuda, “Uriya bai tafi gida ba,” sai Dawuda ya tambaye shi ya ce, “Ba ka zo daga wuri mai nisa ba? Me ya sa ba ka je gida ba?”
11 Et Urie répondit à David: L'arche, et Israël et Juda logent sous des tentes; mon seigneur Joab aussi et les serviteurs de mon seigneur campent aux champs; et moi j'entrerais dans ma maison pour manger et boire, et pour coucher avec ma femme? Tu es vivant, et ton âme vit, que je ne saurais faire une telle chose!
Sai Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin Alkawari, da Isra’ila, da Yahuda suna zama cikin tentuna, kuma maigidana Yowab da mutanen ranka yă daɗe suna a sansani a fili. Yaya zan je gidana in ci in sha in kuma kwana da matata? Muddin kana a raye, ba zan yi irin wannan abu ba!”
12 Et David dit à Urie: Demeure encore ici aujourd'hui, et demain je te renverrai. Urie resta donc à Jérusalem ce jour-là et le lendemain.
Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ƙara dakata a nan kwana ɗaya, gobe kuwa in sallame ka.” Saboda haka Uriya ya dakata a Urushalima a ranar, da kuma ta biye.
13 Puis David l'appela, et il mangea et but devant lui, et David l'enivra; mais le soir il sortit pour coucher dans son lit, avec les serviteurs de son maître, et ne descendit point dans sa maison.
Dawuda ya gayyace shi, ya kuwa ci ya sha tare da shi, Dawuda ya sa ya bugu tilis. Amma da yamma Uriya ya koma ya kwanta a tabarmarsa cikin bayin maigidan sarki; bai je gida ba.
14 Alors, le lendemain matin, David écrivit une lettre à Joab et l'envoya par les mains d'Urie.
Da safe Dawuda ya rubuta wa Yowab wasiƙa ya ba wa Uriya.
15 Or il écrivit en ces termes: Placez Urie à l'endroit où sera le plus fort de la bataille, et retirez-vous d'auprès de lui, afin qu'il soit frappé et qu'il meure.
A ciki wasiƙar ya rubuta, “Tura Uriya a gaba inda yaƙi ya fi zafi. Sa’an nan ka janye daga gare shi don a buge shi yă mutu.”
16 Joab, ayant donc considéré la ville, plaça Urie à l'endroit où il savait que seraient les plus vaillants hommes.
Saboda haka yayinda Yowab ya kai yaƙi kusa da birnin, sai tura Uriya a inda ya sani akwai jarumawan Ammon na gaske.
17 Et ceux de la ville sortirent et combattirent contre Joab, et plusieurs tombèrent parmi le peuple, d'entre les serviteurs de David. Urie, le Héthien, mourut aussi.
Sa’ad da mutanen garin suka fito suka yaƙi Yowab, sai waɗansu mutane daga sojojin Dawuda suka mutu; Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.
18 Puis Joab envoya vers David, pour lui faire savoir tout ce qui était arrivé dans le combat.
Yowab ya aika wa Dawuda cikakken labari batun yaƙin.
19 Et il donna cet ordre au messager, et lui dit: Quand tu auras achevé de parler au roi de tout ce qui est arrivé dans le combat,
Ya umarci manzon ya ce, “Da ka gama yin wa sarki wannan batun yaƙin,
20 S'il arrive que le roi se mette en colère et qu'il te dise: Pourquoi vous êtes-vous approchés de la ville pour combattre? Ne savez-vous pas bien qu'on tire de dessus la muraille?
wataƙila sarki yă husata, yă tambaye ka, ‘Me ya sa kuka je kusa da birnin don ku yi yaƙi? Ba ku san cewa za su yi harbi daga katanga ba?
21 Qui tua Abimélec, fils de Jérubbésheth? N'est-ce pas une femme qui jeta sur lui un morceau de meule de moulin, du haut de la muraille, et il mourut à Thébets? Pourquoi vous êtes-vous approchés de la muraille? Alors tu lui diras: Ton serviteur Urie, le Héthien, est mort aussi.
Wane ne ya kashe Abimelek ɗan Yerub-Beshet? Ba mace ce ta jefa dutsen niƙa a kansa daga katanga, ta haka ya mutu a Tebez ba? Me ya sa kuka je kurkusa da katangar?’ In ya tambaye ka wannan, sai ka ce masa, ‘Har bawanka Uriya mutumin Hitti ma ya mutu.’”
22 Ainsi le messager partit, et, étant arrivé, il fit savoir à David toutes les choses pour lesquelles Joab l'avait envoyé.
Manzon ya tashi ya tafi, da ya iso kuwa sai ya gaya wa Dawuda dukan abin da Yowab ya aike shi yă faɗa.
23 Le messager dit donc à David: Ces gens se sont montrés plus forts que nous, et sont sortis contre nous dans la campagne; mais nous les avons repoussés jusqu'à l'entrée de la porte.
Manzon ya ce wa Dawuda, “Mutanen sun sha kanmu suka fito suka yaƙe mu a fili, amma muka kore su har ƙofar birni.
24 Et les archers ont tiré contre tes serviteurs, du haut de la muraille, et quelques-uns des serviteurs du roi sont morts; ton serviteur Urie, le Héthien, est mort aussi.
Sa’an nan maharba suka yi ta harbi daga katanga har waɗansu mutanen sarki suka mutu. Ban da haka ma, Uriya mutumin Hitti bawan sarki ya mutu.”
25 Et David dit au messager: Tu diras ainsi à Joab: Que cela ne te peine point; car l'épée dévore tantôt l'un, tantôt l'autre; redouble le combat contre la ville, et détruis-la. Et toi, encourage-le!
Dawuda ya ce wa manzon, “Ka gaya wa Yowab, ‘Kada ka bar wannan yă dame ka; yadda takobi ya lamushe wannan, haka zai lamushe wancan ma. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku hallaka shi.’ Ka faɗa haka don ka ƙarfafa Yowab.”
26 Or la femme d'Urie apprit qu'Urie, son mari, était mort, et elle prit le deuil pour son mari.
Da matar Uriya ta ji cewa mijinta ya mutu, sai ta yi makoki saboda shi.
27 Quand le deuil fut passé, David envoya, et la recueillit dans sa maison, et elle fut sa femme, et elle lui enfanta un fils. Mais l'action que David avait faite, déplut à l'Éternel.
Bayan kwanakin makoki suka ƙare, Dawuda ya sa aka kawo ta gidansa, ta kuwa zama matarsa, ta kuma haifa masa ɗa. Sai dai abin da Dawuda ya yi bai gamshi Ubangiji ba.

< 2 Samuel 11 >