< 2 Rois 3 >
1 Joram, fils d'Achab, devint roi d'Israël, à Samarie, la dix-huitième année de Josaphat, roi de Juda, et il régna douze ans.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Il fit ce qui est mauvais aux yeux de l'Éternel, non pas pourtant comme son père et sa mère; car il ôta la statue de Baal que son père avait faite.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Seulement il demeura dans les péchés de Jéroboam, fils de Nébat, qui avait fait pécher Israël. Il ne s'en détourna point.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Or Mésha, roi de Moab, avait de grands troupeaux; et il payait au roi d'Israël un tribut de cent mille agneaux et cent mille béliers avec leur laine.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Mais, aussitôt qu'Achab fut mort, le roi de Moab se révolta contre le roi d'Israël.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 C'est pourquoi le roi Joram sortit en ce jour de Samarie, et fit le dénombrement de tout Israël.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 Et il envoya vers Josaphat, roi de Juda, pour lui dire: Le roi de Moab s'est révolté contre moi. Viendras-tu avec moi à la guerre contre Moab? Et il répondit: J'y monterai; dispose de moi comme de toi, de mon peuple comme de ton peuple, de mes chevaux comme de tes chevaux.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Et il dit: Par quel chemin monterons-nous? Et Joram répondit: Par le chemin du désert d'Édom.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Ainsi le roi d'Israël partit, avec le roi de Juda et le roi d'Édom; et, faisant le tour, ils marchèrent pendant sept jours; mais l'eau manqua pour le camp et pour les bêtes qui suivaient.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Alors le roi d'Israël dit: Hélas! l'Éternel a sûrement appelé ces trois rois pour les livrer entre les mains de Moab
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Et Josaphat dit: N'y a-t-il point ici quelque prophète de l'Éternel, afin que nous consultions l'Éternel par son moyen? Un des serviteurs du roi d'Israël répondit, et dit: Élisée, fils de Shaphat, qui versait l'eau sur les mains d'Élie, est ici.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Et Josaphat dit: La parole de l'Éternel est avec lui. Alors le roi d'Israël, Josaphat et le roi d'Édom descendirent vers lui.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Mais Élisée dit au roi d'Israël: Qu'y a-t-il entre moi et toi? Va-t'en vers les prophètes de ton père et vers les prophètes de ta mère! Et le roi d'Israël répondit: Non! car l'Éternel a appelé ces trois rois pour les livrer entre les mains de Moab.
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Alors Élisée dit: L'Éternel des armées, devant qui je me tiens, est vivant! si je n'avais égard à Josaphat, roi de Juda, je ne ferais point attention à toi, et je ne te regarderais pas.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Mais maintenant, amenez-moi un joueur de harpe. Et comme le joueur de harpe jouait, la main de l'Éternel fut sur Élisée.
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 Et il dit: Ainsi a dit l'Éternel: Qu'on fasse des fossés par toute cette vallée.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Car ainsi parle l'Éternel: Vous ne verrez ni vent ni pluie, et cette vallée se remplira d'eaux et vous boirez, vous, vos troupeaux et vos bêtes.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Et c'est peu de chose aux yeux de l'Éternel: Il livrera encore Moab entre vos mains.
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Et vous frapperez toutes les villes fortes et toutes les villes principales; vous abattrez tous les bons arbres, vous boucherez toutes les sources d'eau, et vous couvrirez de pierres tous les meilleurs champs.
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Le matin donc, à l'heure où l'on offre l'oblation, il arriva qu'on vit des eaux venir par le chemin d'Édom, et le pays fut rempli d'eaux.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Or tous les Moabites, ayant appris que les rois étaient montés pour leur faire la guerre, s'étaient assemblés à cri public, depuis l'âge où l'on ceint le baudrier et au-dessus; et ils se tenaient sur la frontière.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Et, le matin, à leur lever, comme le soleil se levait sur les eaux, les Moabites virent vis-à-vis d'eux les eaux rouges comme du sang.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Et ils dirent: C'est du sang! Certainement, les rois se sont entre-tués, et chacun a frappé son compagnon. Maintenant donc, Moabites, au butin!
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Ainsi, ils vinrent au camp d'Israël; mais les Israélites se levèrent et battirent les Moabites, qui s'enfuirent devant eux; puis ils avancèrent dans le pays, et frappèrent Moab.
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 Ils détruisirent les villes, jetèrent chacun des pierres dans les meilleurs champs, et les remplirent; ils bouchèrent toutes les sources d'eau, et abattirent tous les bons arbres, jusqu'à ne laisser que les pierres à Kir-Haréseth, que les tireurs de fronde environnèrent et battirent.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Et le roi de Moab, voyant qu'il n'était pas le plus fort, prit avec lui sept cents hommes tirant l'épée, pour pénétrer jusqu'au roi d'Édom; mais ils ne le purent.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Alors il prit son fils aîné, qui devait régner à sa place, et il l'offrit en holocauste sur la muraille. Et il y eut chez les Israélites une grande indignation. Ainsi ils se retirèrent de lui, et s'en retournèrent en leur pays.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.