< 2 Rois 11 >

1 Or Athalie, mère d'Achazia, voyant que son fils était mort, se leva et extermina toute la race royale.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 Mais Joshéba, fille du roi Joram, sœur d'Achazia, prit Joas, fils d'Achazia, le déroba d'entre les fils du roi qu'on faisait mourir, et le mit, avec sa nourrice, dans la salle des lits. Ainsi on le cacha aux yeux d'Athalie, en sorte qu'il ne fut pas mis à mort.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 Et il fut caché auprès d'elle, six ans, dans la maison de l'Éternel. Et Athalie régnait sur le pays.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 Et, la septième année, Jéhojada envoya chercher les centeniers des gardes et des coureurs, les fit entrer vers lui dans la maison de l'Éternel, traita alliance avec eux et leur fit prêter serment dans la maison de l'Éternel, et il leur montra le fils du roi.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 Puis il leur donna ce commandement: Voici ce que vous ferez: Un tiers d'entre vous qui entrez en semaine, fera la garde de la maison du roi;
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 Un tiers sera à la porte de Sur; et un tiers à la porte qui est derrière les coureurs. Ainsi vous ferez la garde du temple, afin que personne n'y entre.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 Et vos deux compagnies qui sortent de semaine, feront la garde de la maison de l'Éternel auprès du roi.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 Vous environnerez le roi de tous côtés, chacun tenant ses armes à la main. Celui qui entrera dans les rangs sera mis à mort. Et vous serez avec le roi, quand il sortira et quand il entrera.
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 Les centeniers firent donc tout ce que Jéhojada, le sacrificateur, avait commandé. Ils prirent chacun leurs gens, tant ceux qui entraient en semaine que ceux qui sortaient de semaine; et ils vinrent vers le sacrificateur Jéhojada.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 Et le sacrificateur donna aux centeniers les lances et les boucliers qui provenaient du roi David, et qui étaient dans la maison de l'Éternel.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 Et les coureurs se rangèrent auprès du roi tout à l'entour, chacun tenant ses armes à la main, depuis le côté droit du temple jusqu'au côté gauche, le long de l'autel et du temple.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 Alors il fit sortir le fils du roi, et mit sur lui la couronne et le témoignage. Ils l'établirent roi et l'oignirent, et, frappant des mains, ils dirent: Vive le roi!
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 Mais Athalie, entendant le bruit des coureurs et du peuple, vint vers le peuple, dans la maison de l'Éternel.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 Elle regarda, et voici, le roi était debout près de la colonne, selon la coutume, et les capitaines et les trompettes étaient près du roi; et tout le peuple du pays était dans la joie, et l'on sonnait des trompettes. Alors Athalie déchira ses vêtements, et cria: Conspiration, conspiration!
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 Mais le sacrificateur Jéhojada donna cet ordre aux chefs de centaines, qui commandaient l'armée: Menez-la hors des rangs; et que celui qui la suivra soit mis à mort par l'épée! Car le sacrificateur avait dit: Qu'on ne la fasse pas mourir dans la maison de l'Éternel!
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 On lui fit donc place, et elle revint par le chemin de l'entrée des chevaux dans la maison du roi; elle fut tuée là.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Et Jéhojada traita cette alliance, entre l'Éternel, le roi et le peuple, qu'ils seraient le peuple de l'Éternel; il fit aussi alliance entre le roi et le peuple.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 Alors tout le peuple du pays entra dans la maison de Baal; et ils la démolirent avec ses autels, et ils brisèrent entièrement ses images. Ils tuèrent aussi devant les autels Matthan, sacrificateur de Baal. Ensuite le sacrificateur établit des surveillants dans la maison de l'Éternel.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 Il prit aussi les centeniers, les gardes, les coureurs et tout le peuple du pays, qui firent descendre le roi de la maison de l'Éternel, et ils entrèrent dans la maison du roi par le chemin de la porte des coureurs; et il s'assit sur le trône des rois.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 Tout le peuple du pays se réjouit, et la ville fut en repos, après qu'on eut mis à mort Athalie, par l'épée, dans la maison du roi.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 Joas était âgé de sept ans, quand il devint roi.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Rois 11 >