< 1 Samuel 6 >
1 L'arche de l'Éternel ayant été pendant sept mois au pays des Philistins,
Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
2 Les Philistins appelèrent les sacrificateurs et les devins, et leur dirent: Que ferons nous de l'arche de l'Éternel? Apprenez-nous comment nous la renverrons en son lieu.
Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
3 Et ils répondirent: Si vous renvoyez l'arche du Dieu d'Israël, ne la renvoyez point à vide; mais ne manquez pas de lui payer une offrande pour le délit; alors vous serez guéris, et vous saurez pourquoi sa main ne s'est point retirée de dessus vous.
Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
4 Et ils dirent: Quelle offrande lui payerons-nous pour le délit? Et ils répondirent: D'après le nombre des princes des Philistins, cinq hémorrhoïdes d'or, et cinq souris d'or; car une même plaie a été sur vous tous, et sur vos princes.
Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
5 Vous ferez donc des figures de vos hémorrhoïdes, et des figures des souris qui dévastent le pays, et vous donnerez gloire au Dieu d'Israël; peut-être allégera-t-il sa main de dessus vous, et de dessus vos dieux, et de dessus votre pays.
Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
6 Et pourquoi endurciriez-vous votre cœur, comme les Égyptiens et Pharaon endurcirent le leur? Après qu'il eut accompli contre eux ses prodiges, ne les laissèrent-ils pas partir et s'en aller?
Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
7 Maintenant donc prenez de quoi faire un chariot tout neuf, et deux vaches qui allaitent, sur lesquelles on n'ait point encore mis de joug; et attelez les deux vaches au chariot, et ramenez leurs petits à la maison.
“Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
8 Prenez ensuite l'arche de l'Éternel, et mettez-la sur le chariot; et mettez les ouvrages d'or, que vous lui aurez payés en offrande pour le délit, dans un coffret, à côté d'elle, et renvoyez-la, et qu'elle s'en aille.
Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
9 Puis, regardez; si elle monte vers Beth-Shémesh, par le chemin de sa frontière, c'est l'Éternel qui nous a fait ce grand mal; sinon, nous saurons que sa main ne nous a point touchés, mais que ceci nous est arrivé par hasard.
Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
10 Et ces gens firent ainsi. Ils prirent deux vaches qui allaitaient, et les attelèrent au chariot, et enfermèrent leurs petits dans la maison;
Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
11 Et ils mirent l'arche de l'Éternel sur le chariot, et le coffret, avec les souris d'or et les figures de leurs tumeurs.
Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
12 Alors les vaches prirent tout droit le chemin de Beth-Shémesh, et tinrent toujours la même route, marchant et mugissant; et elles ne se détournèrent ni à droite ni à gauche; et les princes des Philistins allèrent après elles jusqu'à la frontière de Beth-Shémesh.
Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
13 Or, les gens de Beth-Shémesh moissonnaient les blés dans la vallée; et ils levèrent les yeux, et virent l'arche, et se réjouirent de la voir.
A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
14 Et le chariot vint au champ de Josué, de Beth-Shémesh, et s'arrêta là. Or, il y avait là une grande pierre, et on fendit le bois du chariot, et on offrit les vaches en holocauste à l'Éternel;
Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
15 Et les Lévites descendirent l'arche de l'Éternel, et le coffret qui était auprès, dans lequel étaient les ouvrages d'or, et ils les mirent sur la grande pierre. En ce jour, ceux de Beth-Shémesh offrirent des holocaustes et des sacrifices à l'Éternel.
Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
16 Et les cinq princes des Philistins, ayant vu cela, retournèrent le même jour à Ékron.
Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
17 Et voici les tumeurs d'or que les Philistins donnèrent à l'Éternel, en offrande pour le délit; une pour Asdod, une pour Gaza, une pour Askélon, une pour Gath, une pour Ékron.
Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
18 Et il y avait des souris d'or, selon le nombre de toutes les villes des Philistins soumises aux cinq princes, tant des villes fermées que des bourgs sans murailles. Or la grande pierre sur laquelle on posa l'arche de l'Éternel, est encore jusqu'à ce jour dans le champ de Josué de Beth-Shémesh.
Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
19 Et l'Éternel frappa les gens de Beth-Shémesh, parce qu'ils avaient regardé dans l'arche de l'Éternel; et il frappa dans le peuple, soixante et dix hommes, et cinquante mille hommes. Et le peuple fut dans le deuil, parce que l'Éternel l'avait frappé d'une grande plaie.
Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
20 Alors ceux de Beth-Shémesh dirent: Qui pourrait subsister en présence de l'Éternel, de ce Dieu saint? Et vers qui montera-t-il en s'éloignant de nous?
Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
21 Et ils envoyèrent des messagers aux habitants de Kirjath-Jearim, pour leur dire: Les Philistins ont ramené l'arche de l'Éternel; descendez, et faites-la monter vers vous.
Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”