< 1 Samuel 23 >

1 Or, on fit ce rapport à David, et on lui dit: Voilà les Philistins qui font la guerre à Keïla, et qui pillent les aires.
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Et David consulta l'Éternel, en disant: Irai-je, et frapperai-je ces Philistins? Et l'Éternel répondit à David: Va, et tu frapperas les Philistins, et tu délivreras Keïla.
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 Et les gens de David lui dirent: Voici, nous avons peur ici dans le pays de Juda; que sera-ce donc si nous allons à Keïla, contre les troupes des Philistins?
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 C'est pourquoi David consulta encore l'Éternel; et l'Éternel lui répondit, et dit: Lève-toi, descends à Keïla; car je livrerai les Philistins entre tes mains.
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 Alors David s'en alla avec ses gens à Keïla, et combattit les Philistins, et emmena leur bétail, et il en fit un grand carnage; et David délivra les habitants de Keïla.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 Or, quand Abiathar, fils d'Achimélec, s'enfuit vers David à Keïla, il y descendit, ayant l'éphod entre les mains.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 Et on rapporta à Saül que David était venu à Keïla; et Saül dit: Dieu l'a livré entre mes mains; car, en entrant dans une ville qui a des portes et des barres, il s'est enfermé.
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 Et Saül convoqua tout le peuple à la guerre, pour descendre à Keïla, afin d'assiéger David et ses gens.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 Mais David, ayant su que Saül machinait contre lui pour le perdre, dit au sacrificateur Abiathar: Apporte l'éphod.
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 Puis David dit: Éternel, Dieu d'Israël, ton serviteur a entendu dire que Saül cherche à venir contre Keïla, pour détruire la ville à cause de moi;
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 Les chefs de Keïla me livreront-ils entre ses mains? Saül descendra-t-il, comme ton serviteur l'a entendu dire? Éternel, Dieu d'Israël, enseigne-le, je te prie, à ton serviteur. Et l'Éternel répondit: Il descendra.
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 David dit encore: Les chefs de Keïla me livreront-ils, moi et mes gens, entre les mains de Saül? Et l'Éternel répondit: Ils te livreront.
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Alors David se leva avec ses gens, environ six cents hommes, et ils sortirent de Keïla, et s'en allèrent où ils purent; et on rapporta à Saül que David s'était sauvé de Keïla; et il cessa de marcher.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 Or David demeura au désert, dans des lieux forts, et il se tint sur la montagne, au désert de Ziph. Et Saül le cherchait tous les jours; mais Dieu ne le livra point entre ses mains.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 David, voyant donc que Saül était sorti pour chercher sa vie, se tenait au désert de Ziph, dans la forêt.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 Alors Jonathan, fils de Saül, se leva, et s'en alla vers David, à la forêt, et le fortifia en Dieu;
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 Et il lui dit: Ne crains point; car la main de Saül, mon père, ne te trouvera point, mais tu régneras sur Israël, et moi je serai le second après toi; et Saül, mon père, le sait bien aussi.
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 Ils traitèrent donc, tous deux, alliance devant l'Éternel. Et David demeura dans la forêt, et Jonathan retourna en sa maison.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Or, les Ziphiens montèrent vers Saül à Guibea, et lui dirent: David ne se tient-il pas caché parmi nous, dans les lieux forts, dans la forêt, au coteau de Hakila, qui est au midi de la région désolée?
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 Maintenant donc, ô roi, si tu souhaites de descendre, descends et ce sera à nous de le livrer entre les mains du roi.
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 Et Saül dit: Que l'Éternel vous bénisse, de ce que vous avez eu pitié de moi!
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Allez donc, faites encore attention; sachez et reconnaissez le lieu où il a posé son pied, et qui l'y a vu; car on m'a dit qu'il est fort rusé.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 Reconnaissez donc et sachez quelle est, de toutes les retraites, celle où il est caché; puis revenez vers moi, quand vous en serez assurés, et j'irai avec vous. Et s'il est dans le pays, je le chercherai soigneusement dans tous les milliers de Juda.
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 Ils se levèrent donc et s'en allèrent à Ziph, devant Saül; mais David et ses gens étaient au désert de Maon, dans la plaine, au midi de la région désolée.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 Ainsi Saül et ses gens allèrent à la recherche; mais on le rapporta à David, et il descendit le rocher et demeura au désert de Maon. Saül, l'ayant appris, poursuivit David au désert de Maon.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 Et Saül marchait d'un côté de la montagne, et David et ses gens allaient de l'autre côté de la montagne; et David se hâtait de s'en aller de devant Saül. Mais comme Saül et ses gens environnaient David et les siens pour les prendre,
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 Un messager vint vers Saül, et lui dit: Hâte-toi, et viens; car les Philistins se sont jetés sur le pays.
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Alors Saül s'en retourna de la poursuite de David, et s'en alla à la rencontre des Philistins. C'est pourquoi l'on a appelé ce lieu-là, Séla-Hammachlékoth (Rocher des Évasions).
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
29 Puis David monta de là, et demeura dans les lieux forts d'En-Guédi.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.

< 1 Samuel 23 >