< 1 Rois 14 >
1 En ce temps-là, Abija, fils de Jéroboam, devint malade.
A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
2 Et Jéroboam dit à sa femme: Lève-toi maintenant, et déguise-toi, qu'on ne reconnaisse pas que tu es la femme de Jéroboam, et va-t'en à Silo; là est Achija, le prophète; c'est lui qui a dit que je serais roi sur ce peuple.
sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
3 Et prends en ta main dix pains, des gâteaux, et un vase de miel, et entre chez lui; il te déclarera ce qui doit arriver à l'enfant.
Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
4 Et la femme de Jéroboam fit ainsi; elle se leva, et s'en alla à Silo, et elle entra dans la maison d'Achija. Or, Achija ne pouvait voir, car ses yeux étaient obscurcis par la vieillesse.
Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
5 Mais l'Éternel avait dit à Achija: Voici la femme de Jéroboam qui vient pour s'enquérir de toi touchant son fils, parce qu'il est malade. Tu lui diras telles et telles choses. Quand elle entrera, elle fera semblant d'être quelque autre.
Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
6 Aussitôt donc qu'Achija eut entendu le bruit de ses pas, comme elle entrait par la porte, il dit: Entre, femme de Jéroboam; pourquoi fais-tu semblant d'être quelque autre? J'ai mission de t'annoncer des choses dures.
Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
7 Va, dis à Jéroboam: Ainsi a dit l'Éternel, le Dieu d'Israël: Parce que je t'ai élevé du milieu du peuple et que je t'ai établi pour conducteur de mon peuple d'Israël;
Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
8 Et que j'ai déchiré le royaume de la maison de David, et te l'ai donné; mais que tu n'as point été comme David, mon serviteur, qui a gardé mes commandements et marché après moi de tout son cœur, ne faisant que ce qui est droit devant moi;
Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
9 Et que tu as fait plus mal que tous ceux qui ont été avant toi; que tu t'en es allé et t'es fait d'autres dieux et des images de fonte, pour m'irriter, et que tu m'as rejeté derrière ton dos;
Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
10 A cause de cela, voici, je vais faire venir du mal sur la maison de Jéroboam; je retrancherai ce qui appartient à Jéroboam, jusqu'à un seul homme, tant ce qui est serré que ce qui est abandonné en Israël; et je raclerai la maison de Jéroboam comme on racle le fumier, jusqu'à ce qu'il n'en reste plus.
“‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
11 Celui de la maison de Jéroboam qui mourra dans la ville, les chiens le mangeront; et celui qui mourra aux champs sera mangé par les oiseaux des cieux; car l'Éternel a parlé.
Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
12 Toi donc, lève-toi et va-t'en en ta maison; aussitôt que tes pieds entreront dans la ville, l'enfant mourra.
“Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
13 Et tout Israël mènera deuil sur lui et l'ensevelira; car lui seul, de la maison de Jéroboam, entrera au tombeau; parce que l'Éternel, le Dieu d'Israël, a trouvé quelque chose de bon en lui seul, de toute la maison de Jéroboam.
Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
14 Et l'Éternel établira sur Israël un roi qui, en ce jour-là, retranchera la maison de Jéroboam. Et quoi? Même dans peu.
“Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
15 Et l'Éternel frappera Israël, comme quand le roseau est agité dans l'eau; et il arrachera Israël de dessus ce bon pays qu'il a donné à leurs pères; et il les dispersera au delà du fleuve, parce qu'ils se sont fait des emblèmes d'Ashéra, irritant l'Éternel.
Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
16 Et il livrera Israël, à cause des péchés que Jéroboam a commis et qu'il a fait commettre à Israël.
Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
17 Alors la femme de Jéroboam se leva et s'en alla; et elle vint à Thirtsa. Et comme elle mettait le pied sur le seuil de la maison, le jeune garçon mourut;
Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
18 Et on l'ensevelit, et tout Israël mena deuil sur lui, selon la parole que l'Éternel avait prononcée par son serviteur Achija, le prophète.
Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
19 Quant au reste des actions de Jéroboam, comment il fit la guerre et comment il régna, voici, cela est écrit au livre des Chroniques des rois d'Israël.
Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
20 Or, le temps que régna Jéroboam fut de vingt-deux ans; puis il s'endormit avec ses pères, et Nadab son fils régna à sa place.
Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Or Roboam, fils de Salomon, régna en Juda. Il avait quarante et un ans quand il commença à régner, et il régna dix-sept ans à Jérusalem, la ville que l'Éternel avait choisie d'entre toutes les tribus d'Israël, pour y mettre son nom. Sa mère s'appelait Naama, l'Ammonite.
Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
22 Et Juda fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel; et, par les péchés qu'ils commirent, ils émurent sa jalousie plus que leurs pères n'avaient jamais fait.
Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
23 Car ils se bâtirent aussi des hauts lieux, avec des statues et des emblèmes d'Ashéra, sur toutes les hautes collines et sous tous les arbres verts.
Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
24 Il y eut même des prostitués dans le pays; ils imitèrent toutes les abominations des nations que l'Éternel avait chassées devant les enfants d'Israël.
Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
25 Or, il arriva la cinquième année du roi Roboam, que Shishak, roi d'Égypte, monta contre Jérusalem;
A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
26 Il prit les trésors de la maison de l'Éternel, et les trésors de la maison royale; il prit tout; il prit aussi tous les boucliers d'or que Salomon avait faits.
Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
27 Et le roi Roboam fit des boucliers d'airain à la place de ceux-là et les mit entre les mains des chefs des coureurs, qui gardaient la porte de la maison du roi.
Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
28 Et, quand le roi entrait dans la maison de l'Éternel, les coureurs les portaient; puis ils les rapportaient dans la chambre des coureurs.
Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
29 Quant au reste des actions de Roboam et tout ce qu'il fit, n'est-ce pas écrit au livre des Chroniques des rois de Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
30 Or, il y eut toujours guerre entre Roboam et Jéroboam.
Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
31 Et Roboam s'endormit avec ses pères; et il fut enseveli avec eux dans la cité de David. Sa mère s'appelait Naama, l'Ammonite; et Abijam, son fils, régna à sa place.
Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.