< 1 Rois 1 >

1 Or le roi David était vieux, et avancé en âge; et, quoiqu'on le couvrît de vêtements, il ne pouvait se réchauffer.
Sa’ad da Sarki Dawuda ya tsufa ya kuma ƙara shekaru, ba ya iya jin ɗumi ko an rufe shi da abin rufuwa.
2 Alors ses serviteurs lui dirent: Qu'on cherche au roi, mon seigneur, une jeune fille vierge qui se tienne devant le roi et qui en ait soin; et qu'elle dorme en ton sein, afin que le roi, mon seigneur, se réchauffe.
Saboda haka bayinsa suka ce masa, “Bari mu nemi wata budurwa wadda za tă yi wa ranka yă daɗe, sarki hidima, tă kuma kula da shi. Za tă dinga kwanta kusa da ranka yă daɗe, yă ji ɗumi.”
3 On chercha donc dans tout le territoire d'Israël une belle jeune fille, et on trouva Abishag, la Sunamite, qu'on amena au roi.
Suka nemi kyakkyawar yarinya cikin fāɗin Isra’ila, sai suka sami Abishag, mutuniyar Shunam, suka kawo ta wa sarki.
4 Or cette jeune fille était fort belle; et elle avait soin du roi et le servait; mais le roi ne la connut point.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce ƙwarai; ta kuwa lura da sarki, ta kuma yi masa hidima, amma sarki bai yi jima’i da ita ba.
5 Or Adonija, fils de Hagguith, s'éleva, disant: Je régnerai. Et il se procura des chars et des cavaliers, et cinquante hommes qui couraient devant lui.
Adoniya, wanda mahaifiyarsa ce Haggit, ya fito ya ce, “Zan zama sarki.” Saboda haka ya nemi kekunan yaƙi, ya kuma shirya dawakai, tare da mutane hamsin da za su sha gabansa.
6 Mais son père ne voulait point lui donner de chagrin pendant sa vie, ni lui dire: Pourquoi agis-tu ainsi? Lui aussi était fort beau, et sa mère l'avait enfanté après Absalom.
(A duk rayuwarsa mahaifinsa bai taɓa tsawata masa yă ce, “Me ya sa kake yin haka ba?” Shi kuwa mai kyan gani ne ƙwarai, shi ne aka haifa bayan Absalom.)
7 Il s'entendit avec Joab, fils de Tséruja, et avec le sacrificateur Abiathar; et ils embrassèrent le parti d'Adonija.
Adoniya ya haɗa baƙi da Yowab ɗan Zeruhiya da kuma Abiyatar firist, suka kuma ba shi goyon baya.
8 Mais le sacrificateur Tsadok, et Bénaja, fils de Jéhojada, et Nathan, le prophète, et Shimeï, et Réi, et les vaillants hommes de David n'étaient point du parti d'Adonija.
Amma Zadok firist, Benahiya ɗan Yehohiyada, annabi Natan, Shimeyi, Reyi da kuma matsara na musamman na Dawuda ba su bi Adoniya ba.
9 Et Adonija immola des brebis, des bœufs et des veaux gras, auprès de la pierre de Zohéleth, à côté de la fontaine de Roguel; et il convia tous ses frères, les fils du roi, et tous les hommes de Juda qui étaient au service du roi.
Wata rana Adoniya ya tafi Dutsen Zohelet kusa da En Rogel, inda ya yi hadayar tumaki, da shanun noma, da shanun da ake kiwo a gida. Ya kuma gayyaci’yan’uwansa, wato, sauran’ya’yan Sarki Dawuda, tare da dukan dattawan sarki da suka fito daga Yahuda,
10 Mais il ne convia point Nathan, le prophète, ni Bénaja, ni les vaillants hommes, ni Salomon, son frère.
amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benahiya, ko wani daga matsara na musamman, ko kuwa ɗan’uwansa Solomon ba.
11 Alors Nathan parla à Bath-Shéba, mère de Salomon, et lui dit: N'as-tu pas appris qu'Adonija, fils de Hagguith, a été fait roi, sans que David, notre seigneur, le sache?
Sai Natan ya ce wa Batsheba, mahaifiyar Solomon, “Ki san cewa Adoniya, ɗan Haggit, ya zama sarki ba tare da sanin ranka yă daɗe, sarkinmu Dawuda ba?
12 Et maintenant viens, je te prie, et je te donnerai un conseil afin que tu sauves ta vie et la vie de ton fils Salomon.
Yanzu bari in ba ki shawara yadda za ki cece ranki da kuma ran ɗanki Solomon.
13 Va te présenter au roi David, et dis-lui: O roi, mon seigneur, n'as-tu pas fait ce serment à ta servante, en disant: Ton fils Salomon régnera après moi, et c'est lui qui sera assis sur mon trône? Pourquoi donc est-ce Adonija qui règne?
Ki shiga wurin Sarki Dawuda ki ce masa, ‘Ranka yă daɗe sarki, ba ka rantse mini ni baiwarka cewa, “Tabbatacce Solomon ɗanka ne zai zama sarki bayana, yă kuma zauna a kujerar sarautar ba”? To, me ya sa Adoniya ya zama sarki?’
14 Et voici, pendant que tu parleras encore là avec le roi, j'entrerai moi-même après toi et j'achèverai ton discours.
Yayinda kike can kina magana da sarki, zan shiga in kuma tabbatar da abin da kika faɗa.”
15 Bath-Shéba vint donc vers le roi, dans sa chambre. Or le roi était fort vieux, et Abishag, la Sunamite, le servait.
Saboda haka Batsheba ta je don tă ga sarki. A yanzu dai sarki ya tsufa, yana nan kuma a cikin ɗakinsa, inda Abishag mutuniya Shunam take masa hidima.
16 Et Bath-Shéba s'inclina et se prosterna devant le roi; et le roi lui dit: Qu'as-tu?
Batsheba ta rusuna ta kuma durƙusa a gaban sarki. Sai sarki ya tambaye ta ya ce, “Me kike so?”
17 Et elle lui répondit: Mon seigneur, tu as juré, par l'Éternel ton Dieu, à ta servante, en disant: Certainement ton fils Salomon régnera après moi, et il s'assiéra sur mon trône.
Ta ce masa, “Ranka yă daɗe, kai kanka ka rantse mini ni baiwarka da sunan Ubangiji Allahnka cewa, ‘Solomon ɗanka zai zama sarki bayana, zai kuma zauna a kujerar sarautata.’
18 Mais maintenant, voici, c'est Adonija qui est roi, et tu n'en sais rien, ô roi, mon seigneur!
Amma yanzu Adoniya ya zama sarki, kai kuwa ranka yă daɗe sarki, ba ka san wani abu game da shi ba.
19 Il a même immolé des bœufs, des veaux gras et des brebis en grand nombre, et il a convié tous les fils du roi, avec Abiathar, le sacrificateur, et Joab, le chef de l'armée; mais il n'a point invité ton serviteur Salomon.
Ya miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa, ya kuma gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da Abiyatar firist, da Yowab shugaban mayaƙa, amma bai gayyaci Solomon bawanka ba.
20 Et pour toi, ô roi, mon seigneur, les yeux de tout Israël sont sur toi, afin que tu leur déclares qui doit s'asseoir sur le trône du roi, mon seigneur, après lui.
Ranka yă daɗe sarki, idanun dukan Isra’ila suna a kanka, domin su san wa zai zauna a kujerar ranka yă daɗe sarkina, a bayanka.
21 Or, il arrivera, lorsque le roi, mon seigneur, se sera endormi avec ses pères, que nous serons tenus pour coupables, moi et mon fils Salomon.
In ba haka, bayan an binne ranka yă daɗe sarki, tare da kakanninsa, za a wulaƙance ni da Solomon ɗana, kamar masu laifi.”
22 Et voici, elle parlait encore avec le roi, quand Nathan, le prophète, arriva.
Yayinda take cikin magana tare da sarki, sai annabi Natan ya iso.
23 Et on l'annonça au roi, en disant: Voici Nathan, le prophète. Et il se présenta devant le roi et se prosterna en terre devant lui sur son visage.
Sai aka faɗa wa sarki, “Ga annabi Natan.” Da Natan ya je gaban sarki, sai ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
24 Et Nathan dit: O roi, mon seigneur, as-tu dit: Adonija régnera après moi et s'assiéra sur mon trône?
Natan ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki, ko ka furta cewa Adoniya ne zai zama sarki a bayanka, yă kuma zauna a kujerar sarautarka?
25 Car il est descendu aujourd'hui, et il a immolé des bœufs, des veaux gras et des brebis en grand nombre; et il a convié tous les fils du roi, et les chefs de l'armée et le sacrificateur Abiathar; et voici, ils mangent et boivent devant lui, et ils ont dit: Vive le roi Adonija!
Yau ya gangara, ya kuma miƙa hadayun shanu, da shanun da ake kiwo a gida, da tumaki masu yawa. Ya gayyaci dukan’ya’yan sarki maza, da shugaban mayaƙa, da kuma Abiyatar firist. A yanzu haka suna ci, suna sha, tare da shi, suna cewa, ‘Ran Sarki Adoniya yă daɗe!’
26 Mais il n'a convié ni moi, ton serviteur, ni le sacrificateur Tsadok, ni Bénaja, fils de Jéhojada, ni Salomon, ton serviteur.
Amma bai gayyace ni bawanka, da Zadok firist, da Benahiya ɗan Yehohiyada, da kuma bawanka Solomon ba.
27 Ceci aurait-il été fait par le roi, mon seigneur, sans que tu eusses fait savoir à tes serviteurs qui doit s'asseoir sur le trône du roi, mon seigneur, après lui?
Ranka yă daɗe, sarki, ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fadawanka, cewa ga wanda zai gāje Ranka yă daɗe, sarki ba?”
28 Alors le roi David répondit et dit: Appelez-moi Bath-Shéba; et elle se présenta devant le roi et se tint devant lui.
Sai Dawuda ya ce, “Kira Batsheba tă shiga.” Sai ta zo gaban sarki ta kuma tsaya a gabansa.
29 Alors le roi jura, et dit: L'Éternel, qui a délivré mon âme de toute détresse, est vivant!
Sai sarki ya yi rantsuwa, “Muddin Ubangiji yana a raye, wanda ya cece ni daga kowace damuwa,
30 Comme je te l'ai juré par l'Éternel, le Dieu d'Israël, en disant: Certainement ton fils Salomon régnera après moi et s'assiéra sur mon trône à ma place, ainsi ferai-je aujourd'hui.
tabbatacce a yau zan aikata abin da na yi miki rantsuwa da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila; Solomon ɗanki zai zama sarki bayana, kuma shi zai zauna a kan kujerar sarautata a maimakona.”
31 Et Bath-Shéba s'inclina le visage contre terre, et se prosterna devant le roi, et dit: Que le roi David, mon seigneur, vive à jamais!
Sai Batsheba ta rusuna da fuskarta har ƙasa, ta kuma durƙusa a gaban sarki ta ce, “Bari ran Sarkina Dawuda yă daɗe, har abada!”
32 Puis le roi David dit: Appelez-moi Tsadok, le sacrificateur, et Nathan, le prophète, et Bénaja, fils de Jéhojada. Et ils se présentèrent devant le roi.
Sarki Dawuda ya ce, “Ku kira mini Zadok firist, annabi Natan, da Benahiya ɗan Yehohiyada.” Da suka zo gaban sarki,
33 Et le roi leur dit: Prenez avec vous les serviteurs de votre seigneur, et faites monter mon fils Salomon sur ma mule, et faites-le descendre à Guihon;
sai ya ce musu, “Ku ɗauki bayin sarki tare da ku, ku kuma sa ɗana Solomon a kan dokina, ku gangara da shi zuwa Gihon.
34 Et que là Tsadok, le sacrificateur, et Nathan, le prophète, l'oignent roi sur Israël. Ensuite, vous sonnerez de la trompette, et vous direz: Vive le roi Salomon!
A can ku sa Zadok firist, da annabi Natan su shafe shi sarki a bisa Isra’ila. Ku busa ƙaho, ku kuma yi ihu, kuna cewa, ‘Ran Sarki Solomon yă daɗe!’
35 Et vous monterez après lui, et il viendra, et s'assiéra sur mon trône, et régnera à ma place; car j'ai ordonné qu'il soit conducteur d'Israël et de Juda.
Sa’an nan ku haura tare da shi, zai kuwa zo yă zauna a kujera sarautata, yă yi mulki a maimakona. Na naɗa shi mai mulki a bisa Isra’ila da Yahuda.”
36 Alors Bénaja, fils de Jéhojada, répondit au roi et dit: Amen! Que l'Éternel, le Dieu du roi, mon seigneur, l'ordonne ainsi!
Benahiya ɗan Yehohiyada ya amsa wa sarki, ya ce, “Amin! Bari Ubangiji Allah na ranka yă daɗe sarkina, yă tabbatar da haka.
37 Comme l'Éternel a été avec le roi, mon seigneur, qu'il soit de même avec Salomon, et qu'il élève son trône plus que le trône du roi David, mon seigneur!
Kamar yadda Ubangiji ya kasance da ranka yă daɗe, sarki, haka ma bari yă kasance da Solomon, yă kuma mai da kujerar sarautarsa tă fi kujerar sarautar ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, girma!”
38 Puis Tsadok, le sacrificateur, descendit avec Nathan, le prophète, et Bénaja, fils de Jéhojada, et les Kéréthiens et les Péléthiens, et ils firent monter Salomon sur la mule du roi David et le menèrent à Guihon.
Sai Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa suka gangara, suka sa Solomon a kan dokin Sarki Dawuda, suka raka shi zuwa Gihon.
39 Et Tsadok, le sacrificateur, prit dans le tabernacle la corne d'huile, et oignit Salomon. Puis on sonna de la trompette, et tout le peuple dit: Vive le roi Salomon!
Zadok firist ya ɗauki ƙahon mai daga tenti mai tsarki, ya shafe Solomon. Sa’an nan suka busa ƙaho, sai dukan mutane suka yi ihu, suna cewa “Ran Sarki Solomon yă daɗe!”
40 Et tout le monde monta après lui; et le peuple jouait de la flûte, et se livrait à une grande joie, et faisait retentir la terre de ses cris.
Dukan mutane kuwa suka haura suka bi shi, suna busan sarewa, suna farin ciki sosai, har ƙasa ta girgiza saboda sowa.
41 Or Adonija et tous les conviés qui étaient avec lui entendirent ce bruit, comme ils achevaient de manger. Joab aussi entendit le son de la trompette, et dit: Pourquoi ce bruit de la ville en tumulte?
Adoniya tare da dukan baƙin da suke tare da shi kuwa suka ji wannan sa’ad da suke gama bikinsu. Da jin busan ƙaho, sai Yowab ya yi tambaya, ya ce, “Me ya jawo surutu haka a birni?”
42 Comme il parlait encore, voici, Jonathan, fils d'Abiathar le sacrificateur, arriva. Et Adonija lui dit: Entre, car tu es un brave; tu apportes de bonnes nouvelles.
Tun yana cikin magana, sai Yonatan ɗan Abiyatar ya iso. Adoniya ya ce, “Shigo! Ai, mutumin kirki irinka, lalle ka kawo labari mai daɗi ne.”
43 Mais Jonathan répondit, et dit à Adonija: Au contraire. Le roi David, notre seigneur, a établi roi Salomon.
Yonatan ya ce wa Adoniya, “A ina! Ranka yă daɗe, Sarkinmu Dawuda ya naɗa Solomon sarki.
44 Et le roi a envoyé avec lui Tsadok, le sacrificateur, Nathan, le prophète, Bénaja, fils de Jéhojada, et les Kéréthiens et les Péléthiens; et ils l'ont fait monter sur la mule du roi.
Sarki ya aika shi tare da Zadok firist, annabi Natan, Benahiya ɗan Yehohiyada, Keretawa, da Feletiyawa, suka sa shi a kan dokin sarki,
45 Puis Tsadok, le sacrificateur, et Nathan, le prophète, l'ont oint pour roi à Guihon; ils en sont remontés avec joie, et toute la ville s'est émue; c'est là le bruit que vous avez entendu.
Zadok firist kuwa da annabi Natan sun shafe shi sarki a Gihon. Daga can suka haura suna kirari, birni kuwa ta ɓarke da sowa. Surutun da kake ji ke nan.
46 Et Salomon s'est même assis sur le trône royal;
Ban da haka ma, Solomon ne sarki yanzu.
47 Et même les serviteurs du roi sont venus pour bénir le roi David, notre seigneur, en disant: Que Dieu rende le nom de Salomon plus grand que ton nom, et qu'il élève son trône plus que ton trône! Et le roi s'est prosterné sur son lit.
Yanzu haka, fadawa sun zo suna wa ranka yă daɗe, Sarki Dawuda, sam barka, suna cewa, ‘Bari Allahnka yă sa sunan Solomon yă zama sananne fiye da naka, bari kuma sarautarsa tă fi taka girma!’ Sarki kuwa ya rusuna, ya yi sujada a kan gadonsa
48 Et voici ce que le roi a dit: Béni soit l'Éternel, le Dieu d'Israël, qui a donné aujourd'hui, pour être assis sur mon trône, un homme que je vois de mes propres yeux!
ya ce, ‘Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bar idanuna suka ga magāji a kan kujerar sarautata a yau.’”
49 Alors tous les conviés qui étaient avec Adonija, furent dans un grand trouble et se levèrent, et chacun s'en alla de son côté.
A nan fa, dukan baƙin Adoniya suka taso da rawar jiki suka watse.
50 Et Adonija, craignant Salomon, se leva et s'en alla, et saisit les cornes de l'autel.
Amma Adoniya, don tsoron Solomon, ya je ya kama ƙahon bagade ya riƙe.
51 Et on en fit rapport à Salomon, en disant: Voici, Adonija a peur du roi Salomon; et voici, il a saisi les cornes de l'autel, et il a dit: Que le roi Salomon me jure aujourd'hui qu'il ne fera pas mourir son serviteur par l'épée.
Sa’ad da aka faɗa wa Solomon cewa, “Adoniya yana tsoron Sarki Solomon, kuma ya manne wa ƙahonin bagade. Yana cewa, ‘Bari Sarki Solomon yă rantse mini a yau cewa ba zai kashe bawansa da takobi ba.’”
52 Alors Salomon dit: S'il se conduit en homme de bien, il ne tombera pas un de ses cheveux à terre; mais s'il se trouve du mal en lui, il mourra.
Solomon ya amsa ya ce, “In ya nuna kansa mai biyayya, ba gashin kansa da zai fāɗi ƙasa; amma in aka same mugunta a cikinsa, zai mutu.”
53 Et le roi Salomon envoya, et le fit ramener de l'autel; et il vint se prosterner devant le roi Salomon. Et Salomon lui dit: Va-t'en dans ta maison.
Sai Sarki Solomon ya aiki mutane, suka kuma sauko da shi daga bagade. Adoniya kuwa ya zo, ya rusuna wa Sarki Solomon, sai Solomon ya ce, “Tafi gidanka.”

< 1 Rois 1 >