< Romains 8 >

1 Il n'y a donc maintenant aucune condamnation pour ceux qui sont en Christ.
Saboda haka, yanzu babu hukunci don waɗanda suke cikin Kiristi Yesu,
2 En effet, la loi de l'esprit, qui donne la vie en Jésus-Christ, m'a affranchi de la loi du Péché et de la mort; car ce qui était impossible à la loi,
gama ta wurin Kiristi Yesu dokar Ruhu mai ba da rai ta’yantar da ni daga Dokar Musa.
3 parce que la chair la rendait impuissante, Dieu l'a fait: en envoyant, à cause du péché, son propre Fils, dans une chair semblable à la chair de péché, il a prononcé la sentence de mort du Péché dans la chair même,
Gama abin da dokar ba tă iya yi saboda kāsawar mutuntaka ba, Allah ya yi shi sa’ad da ya aiko da Ɗansa a kamannin mutum mai zunubi, don yă zama hadaya ta zunubi. Ta haka, ya hukunta zunubi a cikin mutum mai zunubi.
4 afin que la justice ordonnée par la loi soit réalisée en nous, qui marchons, non selon la chair, mais selon l'esprit.
Ya yi haka domin yă cika bukatun adalcin doka a cikinmu, mu da ba ma rayuwa bisa ga mutuntaka, sai dai bisa ga Ruhu.
5 En effet, ceux qui vivent selon la chair, s'affectionnent aux choses de la chair, tandis que ceux qui vivent selon l'esprit, s'affectionnent aux choses de l'esprit.
Waɗanda suke rayuwa bisa ga mutuntaka sun kafa hankulansu a kan sha’awace-shawa’acen jiki; amma waɗanda suke rayuwa bisa ga Ruhu sun kafa hankulansu a kan abubuwan da Ruhu yake so.
6 Or les affections de la chair, c'est la mort, tandis que les affections de l'esprit, c'est la vie et la paix;
Ƙwallafa rai ga al’amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga al’amuran Ruhu kuwa rai ne da salama;
7 attendu que les affections de la chair sont inimitié contre Dieu, car elles ne sont pas soumises à Dieu, elles ne peuvent même pas se soumettre à Lui.
hankalin mai zunubi na gāba da Allah. Ba ya biyayya da dokar Allah, ba kuwa zai iya yin haka ba.
8 Ceux qui vivent selon la chair ne peuvent plaire à Dieu.
Waɗanda mutuntaka yake mulkinsu ba za su iya su gamshi Allah ba.
9 Pour vous, vous ne vivez pas selon la chair, mais vous vivez selon l'esprit, si toutefois l'Esprit de Dieu habite en vous. Si quelqu'un n'a pas l'Esprit de Christ, il ne lui appartient pas;
Ku kam, ana mulkinku ba ta wurin mutuntaka ba, sai dai ta wurin Ruhu, in Ruhun Allah yana zaune a cikinku. In kuma wani ba shi da Ruhun Kiristi, shi ba na Kiristi ba ne.
10 mais si Christ est en vous, le corps est mort à cause du péché, et l'esprit est vie à cause de la justice.
Amma in Kiristi yana a cikinku, jikinku matacce ne saboda zunubi, duk da haka ruhunku yana a raye saboda adalci.
11 Et si l'Esprit de Celui qui a ressuscité Jésus d'entre les morts habite en vous, Celui qui a ressuscité Christ d'entre les morts, donnera aussi la vie à vos corps mortels, parce que son Esprit habite en vous.
In kuwa Ruhu wannan da ya tā da Yesu daga matattu yana zama a cikinku, shi wanda ya tā da Kiristi daga matattu zai ba da rai ga jikunanku masu mutuwa ta wurin Ruhunsa, wanda yake zama a cikinku.
12 Ainsi donc, mes frères, nous ne sommes point redevables à la chair, pour vivre selon la chair;
Saboda haka’yan’uwa, muna da hakki, amma ba na wanda za mu yi rayuwar mutuntaka da yake so ba.
13 car si vous vivez selon la chair, vous mourrez, mais si, par l'esprit, vous faites mourir les actions auxquelles la chair sollicite, vous vivrez;
Gama in kuna rayuwa bisa ga mutuntaka, za ku mutu; amma in ta wurin Ruhu kuka kashe ayyukan jikin nan, za ku rayu.
14 car tous ceux qui sont conduits par l'Esprit de Dieu, sont fils de Dieu.
Domin waɗanda Ruhun Allah yake bi da su ne’ya’yan Allah.
15 En effet, vous n'avez pas reçu un esprit d'esclavage, pour être encore dans la crainte, mais vous avez reçu un esprit filial, par lequel nous crions: «Abba! Père!»
Gama ba ku karɓi ruhun da ya mai da ku bayi da za ku sāke jin tsoro ba ne, sai dai kun karɓi Ruhun zaman ɗa. Ta wurinsa kuwa muke kira, “Abba, Uba.”
16 Cet esprit même témoigne à notre esprit que nous sommes enfants de Dieu.
Ruhu kansa yana ba da shaida tare da ruhunmu cewa mu’ya’yan Allah ne.
17 — Et, si nous sommes enfants, nous sommes aussi héritiers, héritiers de Dieu et cohéritiers de Christ, si toutefois nous souffrons avec lui, afin d'être aussi glorifiés avec lui.
In kuwa mu’ya’ya ne, to, mu magāda ne, magādan Allah da kuma abokan gādo tare da Kiristi, in kuwa muna tarayya a cikin shan wuyarsa to, za mu yi tarayya a cikin ɗaukakarsa.
18 J'estime que les souffrances du temps présent ne sont rien au prix de la gloire qui nous doit advenir.
A ganina, wuyar da muke sha a wannan lokaci ba su isa a kwatanta da ɗaukakar da za a bayyana a cikinmu ba.
19 Car la Création dans l'attente, attend l'apparition des fils de Dieu:
Halitta tana jira da marmari ta ƙosa ta ga bayyanuwar’ya’yan Allah.
20 en effet, la Création a été assujettie à la vanité — non de son gré, mais par la volonté de Celui qui l'y a soumise —
Gama an sa halitta a cikin wulaƙanci, ba da son ta ba, sai dai ta wurin nufin wannan da ya mai da ita haka, da bege
21 avec l'espérance qu'elle aussi, la Création, sera affranchie de l'esclavage de la corruption, pour avoir part à la liberté de la gloire des enfants de Dieu.
cewa za a’yantar da halitta kanta daga bautarta ga ruɓewa a kuma kawo ta cikin’yancin ɗaukakar’ya’yan Allah.
22 Car nous savons que toute la Création gémit et souffre jusqu’à présent,
Mun san cewa dukan halitta tana nishi sai ka ce mace mai naƙuda har yă zuwa wannan lokaci.
23 et non seulement elle, mais nous-mêmes aussi, quoique nous ayons les prémices de l'Esprit, nous-mêmes aussi, nous gémissons intérieurement, attendant d'être adoptés, délivrés de notre corps.
Ba haka kaɗai ba ma, mu kanmu da muke da nunan fari na Ruhu, muna nishi a ciki-cikinmu yayinda muke jira da marmari a maishe mu’ya’yan riƙo na Allah, fansar jikunanmu.
24 En effet, c'est en espérance que nous sommes sauvés; or, quand on voit ce qu'on espère, ce n'est pas espérance; car espère-t-on encore ce qu'on voit?
Gama a wannan begen ne muka sami ceto. Amma begen da ake gani ba bege ba ne sam. Wa yake begen abin da ya riga ya samu?
25 mais, si nous espérons ce que nous ne voyons pas, nous l'attendons avec patience.
Amma in muna begen abin da ba mu riga mun samu tukuna ba, mukan jira da haƙuri.
26 L'Esprit aussi vient pareillement en aide à notre faiblesse: lorsque nous ne savons que demander, ni comment demander, l'Esprit intercède par de muets soupirs,
Haka nan ma, Ruhu yana taimakonmu cikin rashin ƙarfinmu. Ba mu san abin da ya kamata mu roƙa cikin addu’a ba, amma Ruhu kansa yana roƙo a madadinmu da nishe-nishen da kalmomi ba sa iya bayyanawa.
27 et Celui qui sonde les coeurs, connaît quels sont les désirs de l'Esprit, il sait qu'il intercède, selon Dieu, pour des saints.
Shi kuma wanda yake binciken zukatanmu ya san halin Ruhu, domin Ruhu yana roƙo a madadin tsarkaka bisa ga nufin Allah.
28 Nous savons, d'ailleurs, que toutes choses concourent au bien de ceux qui aiment Dieu, de ceux qui ont été appelés conformément à son plan,
Mun kuma san cewa a cikin dukan abubuwa Allah yana aikata alheri ga waɗanda suke ƙaunarsa, yana waɗanda aka kira bisa ga nufinsa.
29 savoir que ceux qu'il a prédestinés et désignés d'avance pour être semblables à l'image de son Fils, en sorte qu'il soit l'aîné d'un grand nombre de frères,
Gama waɗanda Allah ya rigyasani ya kuma ƙaddara su dace da kamannin Ɗansa, don yă zama ɗan fari cikin’yan’uwa masu yawa.
30 que ceux, dis-je, qu'il a désignés d'avance, il les a aussi appelés, — que ceux qu'il a appelés, il les a aussi justifiés, — que ceux qu'il a justifiés, il les a aussi glorifiés.
Waɗanda kuwa ya ƙaddara, su ne ya kira; waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar; waɗanda ya kuɓutar kuwa, su ne ya ɗaukaka.
31 Que dirons-nous donc à ce propos? Si Dieu est pour nous, qui sera contre nous?
Me za mu ce ke nan game da wannan abu? In Allah yana goyon bayanmu, wa kuwa zai iya gāba da mu?
32 Lui qui n'a pas épargné son propre Fils, mais qui l'a livré à la mort pour nous tous, comment ne nous accordera-t-il pas aussi toutes choses avec lui?
Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai kuma ba mu, tare da shi, dukan abubuwa cikin alherinsa ba?
33 — Qui accusera les élus de Dieu? Dieu les justifie!
Wa zai kawo wani zargi a kan waɗanda Allah ya zaɓa? Allah ne mai kuɓutarwa.
34 — Qui les condamnera? Christ est mort! Bien mieux, il est ressuscité, il est à la droite de Dieu, il intercède pour nous!
Wa zai yi hukunci? Yesu Kiristi ne, wanda ya mutu, fiye da haka ma, shi da aka tā da zuwa rai, yana zaune a hannun dama na Allah yana kuma yin roƙo a madadinmu.
35 — Qui nous arrachera à l'amour de Christ? sera-ce l'affliction, la détresse, la persécution, la faim, le dénûment, le péril, l'épée,
Wane ne zai raba mu da ƙaunar Kiristi? Masifa ce ko wahala ko tsanani ko yunwa ko tsiraici ko hatsari ko takobi?
36 car, «à cause de toi, comme dit l'Ecriture, on nous met à mort tout le jour, on nous tient pour des brebis de boucherie?»
Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Saboda kai ne muke fuskantar mutuwa dukan yini; an ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.”
37 Mais, dans toutes ces calamités, nous sommes plus que vainqueurs par celui qui nous a aimés;
A’a, cikin dukan waɗannan abubuwa mun ma fi masu nasara ta wurin shi wanda ya ƙaunace mu.
38 car je suis assuré que ni la mort, ni la vie, ni anges, ni archanges, ni choses présentes, ni choses à venir,
Gama na tabbata cewa ko mutuwa ko rai, ko mala’iku ko aljanu, ko abubuwa na yanzu ko abubuwa masu zuwa nan gaba, ko ikoki,
39 ni puissances, ni hauteurs, ni abîmes, ni rien au monde, ne pourra nous séparer de l'amour que Dieu nous a témoigné en Jésus-Christ, notre Seigneur!
ko tsayi ko zurfi, ko wani abu dabam cikin dukan halitta da zai iya raba mu da ƙaunar Allah wadda take cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.

< Romains 8 >