< Romains 10 >

1 Mes frères, le voeu de mon coeur et ma prière à Dieu pour eux, c'est qu'ils soient sauvés;
’Yan’uwa, abin da zuciyata take so da kuma addu’ata ga Allah saboda Isra’ilawa shi ne su sami ceto.
2 car je leur rends le témoignage qu'ils ont du zèle pour Dieu, mais c'est un zèle mal éclairé.
Gama na shaida su a kan suna da kishi bin Allah, sai dai kishinsu ba a bisa sani ba.
3 En méconnaissant la justice qui vient de Dieu, et en cherchant à établir leur propre justice, ils ne se sont pas soumis à la justice qui vient de Dieu;
Da yake ba su san adalcin da yake fitowa daga Allah ba suka kuma nemi su kafa nasu, sai suka ƙi miƙa kai ga adalcin Allah.
4 car Christ est la fin de la loi, en vue même de la justice, pour tout homme qui a la foi.
Kiristi shi ne ƙarshen doka domin a sami adalci wa kowane mai bangaskiya.
5 En effet, Moïse caractérise comme suit la justice qui vient de la loi: «Celui qui observera ces commandements, obtiendra la vie;
Musa ya bayyana adalcin da yake ga Doka cewa, “Mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu.”
6 tandis que la Justice qui vient de la foi s'exprime ainsi: «Ne dis pas en ton coeur, «qui montera au ciel?» (c'est en faire descendre Christ)
Amma adalcin da yake ga bangaskiya yana cewa, “Kada ka faɗa a zuciyarka, ‘Wa zai hau sama?’” (wato, don yă sauko da Kiristi),
7 «ni qui descendra dans l’abîme?» (c'est faire monter Christ de chez les morts). (Abyssos g12)
“ko kuwa ‘Wa zai gangara can zurfin ƙasa?’” (wato, don yă hauro da Kiristi daga matattu). (Abyssos g12)
8 Mais que dit-elle? - «Ce qu'elle dit est près de toi, dans ta bouche, dans ton coeur, »
Amma mene ne aka ce? “Maganar tana kusa da kai; tana cikin bakinka da kuma cikin zuciyarka,” wato, maganar bangaskiyan nan da muke shela.
9 c'est la parole de la foi que nous prêchons; elle dit que si ta bouche confesse Jésus pour Seigneur, et que tu croies en ton coeur que Dieu l’a ressuscité des morts, tu seras sauvé.
Cewa in ka furta da bakinka, “Yesu Ubangiji ne,” ka kuma gaskata a zuciyarka cewa Allah ya tā da shi daga matattu, za ka sami ceto.
10 En effet, la foi de coeur conduit à la justice, et la confession débouche, au salut;
Gama da zuciyarka ce kakan gaskata a kuma kuɓutar da kai, da bakinka ne kuma kake furta a kuma cece ka.
11 car l'Écriture dit: «Quiconque a foi en lui, ne sera point confus, »
Kamar yadda Nassi ya ce, “Duk wanda ya gaskata da shi ba zai taɓa shan kunya ba.”
12 Il n'y a pas de distinction entre Juifs et Grecs, parce que ce même Christ est le Seigneur de tous les hommes, étant riche pour tous ceux qui l'invoquent,
Gama ba bambanci tsakanin mutumin Yahuda da mutumin Al’ummai, Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa yana kuma ba da albarka a yalwace ga duk masu kira gare shi,
13 car «quiconque invoquera le nom du Seigneur sera sauvé.»
gama, “Duk wanda ya kira bisa sunan Ubangiji zai sami ceto.”
14 Comment donc invoquera-t-on celui en qui l'on n'a pas encore cru? Et comment croira-t-on en celui dont on n'a pas entendu parler? Et comment en entendra-t-on parler, si quelqu'un ne prêche?
To, ta yaya za su kira ga wanda ba su gaskata ba? Ta yaya kuma za su gaskata wanda ba su taɓa ji ba? Ta yaya kuma za su ji ba tare da wani ya yi musu wa’azi ba?
15 Et comment prêchera-t-on, si quelqu'un n'est envoyé, selon qu'il est écrit: «Qu'ils sont beaux les pieds de ceux qui annoncent la paix, de ceux qui annoncent les bonnes nouvelles?
Kuma ta yaya za su yi wa’azi in ba an aike su ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Isowar masu kawo labari mai daɗi abu mai kyau ne ƙwarai!”
16 — Mais tous ne l'ont pas écoutée, la bonne nouvelle, car Ésaïe dit: «Seigneur, qui a ajouté foi à notre prédication?»
Amma ba dukan Isra’ilawa ne suka karɓi labari mai daɗin nan ba. Gama Ishaya ya ce, “Ubangiji, wa ya gaskata saƙonmu?”
17 Ainsi donc, la foi vient de ce qu'on entend, et l'on entend par l'ordre de Dieu.
Saboda haka, bangaskiya takan zo ne ta wurin jin saƙo, akan ji saƙon kuma ta wurin maganar Kiristi.
18 Mais je demande: «N'auraient-ils pas entendu prêcher?» - Ah! bien au contraire; «la voix des messagers a retenti par toute la terre, et leurs paroles sont parvenues jusqu'aux extrémités du monde.»
Amma ina tambaya, “Ba su ji ba ne? Tabbatacce sun ji. “Muryarsu ta tafi ko’ina a cikin duniya, kalmominsu kuma har iyakar duniya.”
19 Je demande encore: «Israël n'aurait-il pas eu connaissance de l’ordre de Dieu?» — Moïse, le premier, a dit: «Je vous rendrai jaloux d'une nation qui n'en est pas une; je provoquerai votre colère contre une nation sans intelligence; »
Har wa yau, ina da tambaya. Shin, Isra’ila ba su fahimta ba ne? Da farko, Musa ya ce, “Zan sa ku yi kishin waɗanda ba al’umma ba; zan sa ku yi fushin al’ummar da ba ta da fahimta.”
20 et Esaïe va même jusqu’à dire: «Je me suis laissé trouver par ceux qui ne me cherchaient point; je me suis fait connaître à ceux qui ne me demandaient point; »
Ishaya kuma ya fito gabagadi ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni; Na bayyana kaina ga waɗanda ba su ma taɓa neman sanina ba.”
21 tandis qu'il dit en parlant d'Israël: «J'ai tout le jour tendu les bras à un peuple rebelle et récalcitrant.»
Amma game da Isra’ila ya ce, “Dukan yini na miƙa hannuwana ga mutane marasa biyayya da masu taurinkai.”

< Romains 10 >