< Jean 6 >
1 Jésus s'en alla ensuite de l'autre côté de la mer de Tibériade en Galilée;
Ɗan lokaci bayan wannan, sai Yesu ya ƙetare zuwa gaɓar mai nesa na Tekun Galili (wato, Tekun Tibariya),
2 et une foule nombreuse le suivait, parce qu'elle voyait les miracles qu'il opérait sur les malades.
sai taro mai yawa na mutane suka bi shi domin sun ga abubuwan banmamakin da ya yi ga marasa lafiya.
3 Jésus monta sur la montagne, et s'y assit avec ses disciples.
Sa’an nan Yesu ya hau gefen dutse ya zauna tare da almajiransa.
4 Or, la Pâque, la grande fête des Juifs, était proche.
Bikin Ƙetarewan Yahudawa ya yi kusa.
5 Jésus donc ayant levé les yeux, et voyant qu'une grande foule se dirigeait de son côté, dit à Philippe: «où nous faut-il acheter du pain, pour que ces gens aient à manger?»
Sa’ad da Yesu ya ɗaga kai ya ga taro mai yawa suna zuwa wajensa, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayi burodi saboda mutanen nan su ci?”
6 Il disait cela pour l'éprouver; car, pour lui, il savait bien ce qu'il voulait faire.
Ya yi wannan tambayar don yă gwada shi ne kawai, gama ya riga ya san abin da zai yi.
7 Philippe lui répondit: «Deux cents deniers de pain ne suffiraient pas pour en donner un peu à chacun.»
Sai Filibus ya amsa ya ce, “Kai, ko albashin wata takwas ba zai iya sayan isashen burodin da kowa zai ɗan samu kaɗan ba!”
8 Un de ses disciples, André, frère de Simon-Pierre, lui dit:
Sai wani daga cikin almajiransa Andarawus, ɗan’uwan Bitrus, ya yi magana,
9 «Il y a ici un petit garçon qui a cinq pains d'orge et deux poissons; mais qu'est-ce que cela pour tant de monde.»
“Ga wani yaro da ƙananan burodin sha’ir guda biyar da ƙananan kifi biyu, amma me wannan zai yi wa yawan mutanen nan.”
10 Jésus dit: «Faites asseoir ces gens.» Or il y avait une grande étendue d'herbe en ce lieu. Les hommes s'assirent donc: ils étaient au nombre d'environ cinq mille.
Yesu ya ce, “Ku sa mutanen su zauna.” Wurin kuwa akwai ciyawa da sosai, sai maza suka zazzauna, sun kai wajen dubu biyar.
11 Jésus prit les pains, et, ayant rendu grâces, il les distribua à ceux qui étaient assis; il leur donna de même des poissons, autant qu'ils en voulurent.
Sa’an nan Yesu ya ɗauki burodin, ya yi godiya, ya kuma rarraba wa waɗanda suke zaune gwargwadon abin da ya ishe su. Haka kuma ya yi da kifin.
12 Lorsqu'ils furent rassasiés, il dit à ses disciples: «Ramassez les morceaux qui restent, afin que rien ne se perde.»
Sa’ad da duk suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka rage. Kada kome yă lalace.”
13 Ils les ramassèrent, et remplirent douze corbeilles des morceaux qui restèrent des cinq pains d'orge, après que l'on eut mangé.
Saboda haka suka tattara su suka kuma cika kwanduna goma sha biyu na gutsattsarin burodin sha’ir biyar nan da suka ragu bayan kowa ya ci.
14 Ces gens ayant vu le miracle que Jésus avait fait, disaient: «C'est vraiment le prophète qui doit venir dans le monde.»
Bayan mutanen suka ga abin banmamakin da Yesu ya yi, sai suka fara cewa, “Lalle, wannan shi ne Annabin nan mai zuwa duniya.”
15 Alors Jésus ayant compris qu'ils allaient venir l'enlever pour le faire roi, se retira de nouveau dans la montagne, tout seul.
Da Yesu ya gane suna shirin su ɗauke shi ƙarfi da yaji su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa kan dutsen shi kaɗai.
16 Quand le soir fut venu, ses disciples descendirent au bord de la mer;
Da yamma ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa tafki,
17 et, étant entrés dans la barque, ils traversèrent la mer dans la direction de Capernaoum. Il faisait déjà nuit, et Jésus ne les avait pas rejoints;
inda suka shiga jirgin ruwa suka tasar wa haye tafkin zuwa Kafarnahum. A lokacin kuwa duhu ya yi, Yesu kuma bai riga ya zo wurinsu ba tukuna.
18 et un gros vent s'étant levé, la mer était agitée.
Iska mai ƙarfi kuwa tana bugowa, ruwaye kuma suka fara hauka.
19 Quand ils eurent fait de vingt-cinq à trente stades, ils virent Jésus marchant sur la mer, près de la barque, et ils eurent peur.
Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko uku da rabi, sai suka ga Yesu ya kusato jirgin ruwan, yana takawa a kan ruwan; sai suka tsorata.
20 Mais Jésus leur dit: «C'est moi, n'ayez point de peur.»
Amma ya ce musu, “Ni ne; kada ku ji tsoro.”
21 Ils se disposèrent donc à le prendre dans la barque, et aussitôt la barque aborda au lieu où ils se rendaient.
Sa’an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin ruwan, nan da nan kuwa jirgin ya kai gaɓar da za su.
22 La foule qui était restée de l'autre côté de la mer avait vu qu'il n'y avait là qu'une seule barque, et que Jésus n'y était point entré avec ses disciples, mais que ceux-ci étaient partis seuls.
Kashegari taron da suka tsaya a wancan ƙetaren tafkin suka lura cewa jirgin ruwa ɗaya ne yake a can dā ma, kuma sun lura cewa Yesu bai shiga ciki tare da almajiransa ba, gama sun tashi su kaɗai.
23 Cependant il était arrivé de Tibériade d'autres barques, près du lieu où ils avaient mangé le pain, après que le Seigneur eut rendu grâces.
Sai ga waɗansu jiragen ruwa daga Tibariya suka iso kusa da wurin da mutanen suka ci burodi bayan Ubangiji ya yi godiya.
24 Le lendemain donc, lorsqu'ils virent que Jésus n'était pas là, non plus que ses disciples, ils entrèrent dans ces barques et se rendirent à Capernaoum pour chercher Jésus.
Da taron suka lura cewa Yesu da almajiransa ba sa can, sai suka shiga jiragen ruwa suka tafi Kafarnahum neman Yesu.
25 Et l'ayant trouvé de l'autre côté de la mer, ils lui dirent: «Maître, quand es-tu venu ici?»
Da suka same shi a wancan ƙetaren tafkin, sai suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, yaushe ka kai nan?”
26 Jésus leur répondit: «En vérité, en vérité, je vous le dis, vous me cherchez, non parce que vous avez vu des miracles, mais parce que vous avez mangé des pains, et que vous avez été rassasiés.
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga abubuwan banmamaki ba, sai dai domin kun ci burodi kun ƙoshi.
27 Travaillez pour avoir, non l'aliment qui périt, mais l'aliment qui subsiste en vie éternelle, et que le Fils de l'homme vous donnera, car c'est lui que le Père, savoir Dieu, a marqué de son sceau.» (aiōnios )
Kada ku yi aiki saboda abincin da yake lalacewa, sai dai saboda abinci mai dawwama har yă zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. A kansa ne Allah Uba ya sa hatimin amincewarsa.” (aiōnios )
28 Ils lui dirent donc: «Que devons-nous faire, pour faire les oeuvres de Dieu?»
Sai suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi don mu aikata ayyukan da Allah yake so?”
29 Jésus leur répondit: «L'oeuvre que Dieu demande, c'est que vous croyiez en celui qu'il a envoyé.»
Yesu ya amsa, “Aikin Allah shi ne, a gaskata da wanda ya aiko.”
30 — Quel miracle fais-tu donc, lui dirent-ils, que nous le voyions, et que nous croyions en toi? Que fais-tu?
Sai suka tambaye shi, “Wace abin banmamaki ce za ka yi don mu gani mu kuwa gaskata ka? Me za ka yi?
31 Nos pères ont mangé la manne au désert, ainsi qu'il est écrit: «Il leur donna à manger du pain du ciel.»
Kakannin-kakanninmu sun ci Manna a hamada; kamar yadda yake a rubuce, ‘Ya ba su burodi daga sama su ci.’”
32 Jésus leur répondit: «En vérité, en vérité, je vous le dis, Moïse ne vous a point donné «le pain du ciel; » c'est mon Père qui vous donne le vrai pain du ciel,
Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba Musa ne ya ba ku burodi daga sama ba, sai dai Ubana ne yake ba ku burodi na gaskiya daga sama.
33 car le pain de Dieu, c'est le pain qui descend du ciel et qui donne la vie au monde.»
Gama burodin Allah shi ne wanda yake saukowa daga sama, yana kuma ba wa duniya rai.”
34 Ils lui dirent donc: «Seigneur, donne-nous toujours de ce pain-là.»
Sai suka ce, “Ranka yă daɗe, daga yanzu ka dinga ba mu wannan burodi.”
35 Jésus leur dit: «Je suis le pain de vie: celui qui vient à moi n'aura jamais faim, et celui qui croit en moi n'aura jamais soif;
Sa’an nan Yesu ya furta cewa, “Ni ne burodin rai. Wanda ya zo wurina ba zai taɓa jin yunwa ba, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai taɓa jin ƙishirwa ba.
36 mais, je vous l'ai dit, vous m'avez vu, et vous ne croyez point.
Amma kamar yadda na faɗa muku, kun gan ni duk da haka ba ku gaskata ba.
37 Tout ce que le Père me donne viendra à moi, et je ne repousserai point celui qui vient à moi;
Duk waɗanda Uba ya ba ni za su zo wurina, kuma duk wanda ya zo wurina ba zan kore shi ba ko kaɗan.
38 car je suis descendu du ciel pour faire, non ma volonté, mais la volonté de celui qui m'a envoyé.
Gama na sauko daga sama ba don in cika nufin kaina ba sai dai don in cika nufin shi wanda ya aiko ni.
39 Or, la volonté de celui qui m'a envoyé, c'est que je ne perde aucun de ceux qu'il m'a donnés, mais que je les ressuscite au dernier jour.
Nufin wanda ya aiko ni kuwa shi ne, kada in yar da ko ɗaya daga cikin duk waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a rana ta ƙarshe.
40 Car c'est ici la volonté de mon Père, que quiconque voit le Fils et croit en lui, ait la vie éternelle; et moi je le ressusciterai au dernier jour.» (aiōnios )
Gama nufin Ubana shi ne, duk wanda yake duban Ɗan, ya kuma gaskata shi zai sami rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.” (aiōnios )
41 Les Juifs se mirent donc à murmurer contre lui, parce qu'il avait dit: «Je suis le pain qui est descendu du ciel, »
Da jin haka, Yahudawa suka fara gunaguni a kansa, domin ya ce, “Ni ne burodin da ya sauka daga sama.”
42 et ils disaient: «N'est-ce pas là Jésus, le fils de Joseph, dont nous connaissons le père et la mère? comment donc dit-il: «Je suis descendu du ciel?»
Suka ce, “Kai, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusuf, wanda mahaifinsa da mahaifiyarsa duk mun san su? Yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko daga sama?’”
43 Jésus répondit et leur dit: «Ne murmurez point entre vous.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ku daina gunaguni a junanku.
44 Nul ne peut venir à moi, si le Père, qui m'a envoyé, ne l'attire; et moi, je le ressusciterai au dernier jour.
Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uban da ya aiko ni ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe.
45 Il est écrit dans les Prophètes: «Et ils seront tous enseignés de Dieu» quiconque a entendu le Père et a profité, vient à moi;
A rubuce yake a cikin Annabawa cewa, ‘Allah zai koyar da dukansu.’Duk wanda ya saurari Uba, ya kuma koyi daga wurinsa, zai zo wurina.
46 ce n'est pas que personne ait vu le Père, si ce n'est celui qui vient de Dieu: celui-là a vu le Père.
Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda ya zo daga Allah; shi ne kaɗai ya taɓa ganin Uban.
47 En vérité, en vérité, je vous le dis, celui qui croit en moi a la vie éternelle. (aiōnios )
Gaskiya nake gaya muku, wanda ya gaskata yana da rai madawwami. (aiōnios )
48 Je suis le pain de vie.
Ni ne burodin rai.
49 Vos pères ont mangé la manne au désert, et ils sont morts;
Kakannin-kakanninku sun ci Manna a hamada, duk da haka suka mutu.
50 quant au pain qui descend du ciel, on en mange et l’on ne meurt point.
Amma ga burodin da ya sauko daga sama, wanda mutum zai iya ci, ba zai kuma mutu ba.
51 Je suis le pain vivifiant qui est descendu du ciel: si quelqu'un mange de ce pain, il vivra éternellement; et le pain que je donnerai, c'est ma chair, que je donnerai pour la vie du monde.» (aiōn )
Ni ne burodin rai mai saukowa daga sama. Duk wanda ya ci wannan burodi, zai rayu har abada. Wannan burodin shi ne jikina, da zan bayar don duniya ta sami rai.” (aiōn )
52 Là-dessus, les Juifs disputaient entre eux, disant: «Comment cet homme peut-il nous donner sa chair à manger?»
Sai Yahudawa suka fara gardama mai tsanani a junansu suna cewa, “Yaya wannan mutum zai ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Jésus leur dit donc: «En vérité, en vérité, je vous le dis, si vous ne mangez la chair du Fils de l'homme, et si vous ne buvez son sang, vous n'avez point la vie en vous-mêmes:
Sai Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, sai kun ci naman jikin Ɗan Mutum kuka kuma sha jininsa, ba za ku kasance da rai a cikinku ba.
54 celui qui mange ma chair et qui boit mon sang a la vie éternelle; et moi, je le ressusciterai au dernier jour. (aiōnios )
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana da rai madawwami. Ni kuwa zan tashe shi a rana ta ƙarshe. (aiōnios )
55 Car ma chair est vraiment une nourriture, et mon sang est vraiment un breuvage.
Gama naman jikina abinci ne na gaskiya jinina kuma abin sha ne na gaskiya.
56 Celui qui mange ma chair et qui boit mon sang demeure en moi, et moi en lui.
Duk wanda ya ci naman jikina ya kuma sha jinina, yana cikina, ni kuma ina cikinsa.
57 Comme le Père, qui a la vie, m'a envoyé, et que je vis par le Père, de même celui qui me mange, vivra par moi.
Kamar dai yadda Uba mai rai ya aiko ni, ina kuma rayuwa ta saboda shi, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni.
58 C'est là le pain qui est descendu du ciel: il n'en est point comme de nos pères qui ont mangé et sont morts; celui qui mange de ce pain vivra éternellement.» (aiōn )
Wannan shi ne burodin da ya sauko daga sama. Kakannin-kakanninku sun ci Manna suka kuma mutu, amma duk wanda yake cin wannan burodi zai rayu har abada.” (aiōn )
59 Jésus dit ces choses, enseignant en pleine synagogue à Capernaoum.
Ya faɗi wannan ne lokacin da yake koyarwa a cikin majami’a a Kafarnahum.
60 Plusieurs de ses disciples, l'ayant entendu, dirent: «Cette parole est dure, qui peut l'écouter?»
Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan koyarwa tana da wuya. Wa zai iya yarda da ita?”
61 Mais Jésus, sachant en lui-même que ses disciples murmuraient, leur dit: «Cela vous scandalise?...
Da yake ya san almajiransa suna gunaguni game da wannan, sai Yesu ya ce musu, “Wannan ya ɓata muku rai ne?
62 que sera-ce donc, si vous voyez le Fils de l’homme monter là où il était auparavant?
Me za ku ce ke nan, in kuka gan Ɗan Mutum yana hawa zuwa inda yake dā!
63 C'est l'esprit qui vivifie; la chair ne sert de rien. Les paroles que je vous ai adressées sont esprit et vie;
Ruhu ne yake ba da rai; jikin kam, ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku, Ruhu ne, da kuma rai.
64 mais il y en a parmi vous qui ne croient point.» En effet, Jésus savait dès l'abord qui étaient ceux qui ne croyaient pas, et qui était celui qui le livrerait.
Duk da haka akwai waɗansunku da ba su gaskata ba.” Gama Yesu ya sani tun farko, waɗanda ba su gaskata ba, da kuma wanda zai bashe shi.
65 Et il ajouta: «C'est pour cela que je vous ai dit que nul ne peut venir à moi, s'il ne lui a été donné du Père.»
Ya ci gaba da cewa, “Shi ya sa na faɗa muku cewa ba mai iya zuwa wurina, sai dai Uba ya yardar masa.”
66 Dès lors plusieurs de ses disciples se retirèrent d'auprès de lui et cessèrent de le suivre.
Daga wannan lokaci da yawa daga cikin almajiransa suka ja da baya, suka daina bin sa.
67 Jésus dit donc aux Douze: «Et vous, ne voulez-vous pas aussi vous en aller?»
Sai Yesu ya tambayi Sha Biyun, “Ku ma za ku tafi ne?”
68 Simon-Pierre lui répondit: «Seigneur, à qui irions-nous? Tu as les paroles de la vie éternelle; (aiōnios )
Sai Siman Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji wajen wa za mu tafi? Kai ne da kalmomin rai madawwami. (aiōnios )
69 pour nous, nous avons cru et nous avons connu, que tu es le Saint de Dieu.»
Mun gaskata mun kuma san cewa kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.”
70 Jésus leur répondit: «N'est-ce pas moi qui vous ai choisis, vous Douze?... et l'un de vous est un démon!»
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ba ni na zaɓe ku Sha Biyu ba? Amma ɗayanku Iblis ne!”
71 Or il parlait de Judas, fils de Simon Iscariote, car c'était lui, l'un des Douze, qui devait le livrer.
(Yana nufin Yahuda, ɗan Siman Iskariyot, wanda, ko da yake ɗaya ne cikin Sha Biyun, zai bashe shi daga baya.)