< Jean 5 >
1 Après cela, il y eut une fête des Juifs, et Jésus monta à Jérusalem.
Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
2 Or il y a à Jérusalem, près de la porte des Brebis, une piscine appelée en hébreu Bethesda, qui a cinq portiques.
To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
3 Là étaient couchés par terre un grand nombre de malades, des aveugles, des boiteux, des gens ayant quelque membre sec. [qui attendaient le bouillonnement de l'eau]
A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
4 [Car un ange descendait, à certains moments, dans la piscine et agitait l'eau. Le premier donc qui entrait dans l'eau, après qu'elle avait été agitée, était guéri de sa maladie, quelle qu'elle fût.]
5 Il y avait là un homme qui était malade depuis trente-huit ans.
Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
6 Jésus le voyant couché, et reconnaissant qu'il était malade depuis longtemps, lui dit: «Tu veux être guéri?»
Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
7 Le malade lui répondit: «Seigneur, je n'ai personne pour me jeter dans la piscine quand l'eau est agitée, et, pendant que j'y vais, un autre descend avant moi.»
Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
8 Jésus lui dit: «Lève-toi, prends ton lit et marche.»
Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
9 Aussitôt cet homme fut guéri: il prit son lit et se mit à marcher. Or c'était un jour de sabbat.
Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
10 Les Juifs dirent donc à celui qui avait été guéri: «C'est le sabbat, il ne t'est pas permis de porter ton lit.»
saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
11 Il leur répondit: «Celui qui m'a guéri m'a dit: «Prends ton lit, et marche.»
Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
12 Ils lui demandèrent: «Qui est cet homme qui t'a dit: Prends et marche?»
Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
13 Mais le malade l'ignorait, car Jésus s'était esquivé, grâce à la foule qui était en cet endroit.
Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
14 Plus tard, le trouvant dans le temple, Jésus lui dit: «Te voilà guéri, ne pèche plus, de peur qu'il ne t'arrive quelque chose de pis.»
Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
15 Cet homme alla rapporter aux Juifs que c'était Jésus qui l'avait guéri.
Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
16 Aussi les Juifs persécutaient-ils Jésus, parce qu'il faisait ces choses le jour du sabbat.
To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
17 Mais Jésus leur répondit: «Mon Père agit continuellement, et moi aussi, j'agis.»
Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
18 C'est pourquoi les Juifs cherchaient encore plus à le faire mourir, non-seulement parce qu'il violait le sabbat, mais encore parce qu'il disait que Dieu était son propre Père, se faisant égal à Dieu.
Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
19 Jésus prenant la parole, leur dit: «En vérité, en vérité, je vous dis que le Fils ne peut rien faire de lui-même, s'il ne le voit faire au Père; car ce que le Père fait, le Fils aussi le fait pareillement.
Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
20 Le Père aime le Fils et lui montre tout ce qu'il fait; et il lui montrera des oeuvres plus grandes que celles-là, afin que vous soyez dans l'étonnement.
Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
21 Car, de même que le Père ressuscite les morts et donne la vie, de même le Fils donne la vie à qui il veut.
Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
22 Le Père même ne juge personne, mais il a remis au Fils le jugement tout entier, afin que tous honorent le Fils comme ils honorent le Père.
Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
23 Celui qui n'honore point le Fils, n'honore point le Père qui l'a envoyé.
don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
24 En vérité, en vérité, je vous le dis, celui qui écoute ma parole, et qui croit en celui qui m'a envoyé, a la vie éternelle; et il n'est point amené en jugement, mais il est passé de la mort à la vie. (aiōnios )
“Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios )
25 En vérité, en vérité, je vous le dis, l'heure vient, et elle est déjà venue, où les morts entendront la voix du Fils de Dieu, et ceux qui l'auront entendue vivront;
Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
26 car, de même que le Père a la vie en lui-même, de même il a donné au Fils d'avoir la vie en lui-même.
Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
27 Il lui a même donné le pouvoir d'exercer le jugement, parce qu'il est un fils d'homme.
Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
28 Ne vous en étonnez point, car l'heure vient, où tous ceux qui sont dans les sépulcres entendront sa voix, et en sortiront:
“Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
29 ceux qui auront fait le bien ressusciteront pour la vie, ceux qui auront fait le mal ressusciteront pour la condamnation.
su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
30 Je ne puis rien faire de moi-même; je juge selon que j'entends; et mon jugement est juste, parce que je ne cherche pas ma volonté, mais la volonté de celui qui m'a envoyé.
Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
31 Si c'est moi qui rends témoignage de moi-même, mon témoignage n'est pas vrai.
“In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
32 Il y en a un autre qui rend témoignage de moi, et je sais que le témoignage qu'il me rend est vrai.
Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
33 Vous avez envoyé vers Jean, et il a rendu témoignage à la vérité.
“Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
34 Pour moi, je n'emprunte pas le témoignage d'un homme, mais ce que je vous en dis. c'est afin que vous soyez sauvés.
Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
35 Jean était la lampe qui brûle et luit, mais vous n'avez voulu vous réjouir qu'un moment à sa lumière.
Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
36 Pour moi, j'ai un témoignage qui est supérieur à celui de Jean, ce sont les oeuvres que mon Père m'a donné d'accomplir: ces oeuvres mêmes rendent témoignage de moi, elles attestent que mon Père m'a envoyé.
“Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
37 Et le Père, qui m'a envoyé, a rendu lui-même témoignage de moi: sa voix, vous ne l'avez jamais entendue; sa face, vous ne l'avez jamais vue;
Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
38 et sa parole... vous ne la gardez pas en vous, puisque vous ne croyez pas en celui qu'il a envoyé.
maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39 Vous sondez les Écritures, parce que vous pensez y trouver la vie éternelle, et ce sont elles qui rendent témoignage de moi; (aiōnios )
Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios )
40 mais vous ne voulez pas venir à moi pour avoir la vie.
duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
41 Je ne demande pas ma gloire aux hommes;
“Ni ba na neman yabon mutane,
42 mais je vous connais, je sais que vous n'avez pas en vous l'amour de Dieu.
na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
43 Je suis venu au nom de mon Père, et vous ne me recevez pas; si un autre vient en son propre nom, vous le recevrez.
Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
44 Comment pouvez-vous croire, vous qui tirez votre gloire les uns des autres et qui ne recherchez pas la gloire qui vient de Dieu seul.
Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
45 Ne pensez pas que ce soit moi qui doive vous accuser devant le Père; votre accusateur, c'est Moïse, en qui vous avez mis votre espérance,
“Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
46 car si vous croyiez Moïse, vous me croiriez, parce qu'il a parlé de moi;
Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
47 mais si vous n'ajoutez pas foi à ses écrits, comment ajouteriez-vous foi à mes paroles?»
Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”