< Actes 4 >
1 Comme Pierre et Jean haranguaient la foule, survinrent les sacrificateurs, le commandant du temple et les sadducéens,
Sai firistoci da shugaban masu gadin haikalin da kuma Sadukiyawa suka hauro wurin Bitrus da Yohanna yayinda suke cikin magana da mutane.
2 fatigués de ce qu'ils enseignaient le peuple et annonçaient, en la personne de Jésus, la résurrection des morts:
Sun damu ƙwarai da gaske domin manzannin suna koya wa mutane suna kuma shela a cikin Yesu cewa akwai tashin matattu.
3 ils les arrêtèrent et les mirent en prison jusqu'au lendemain, car c'était déjà le soir.
Sai suka kama Bitrus da Yohanna, amma da yake yamma ta riga ta yi sai suka sa su cikin kurkuku sai kashegari.
4 Toutefois un grand nombre de ceux qui avaient entendu ce discours, crurent, en sorte que le nombre des hommes s'éleva à environ cinq mille.
Amma da yawa da suka ji saƙon suka gaskata, yawan mutanen kuwa ya ƙaru ya kai wajen dubu biyar.
5 Le lendemain, les magistrats des Juifs, soit anciens, soit scribes,
Kashegari, sai masu mulki, dattawa da kuma malaman dokoki suka taru a Urushalima.
6 et notamment Anne souverain sacrificateur, Caïphe, Jean, Alexandre, et tous ceux qui étaient de la famille des souverains sacrificateurs, s'assemblèrent à Jérusalem,
Annas babban firist yana nan, haka ma Kayifas Yohanna, Alekzanda da kuma sauran mutanen da suke iyalin babban firist.
7 et ayant fait comparaître les apôtres devant eux, ils leur demandèrent: «Par quelle puissance, ou au nom de qui avez-vous fait cela?»
Suka sa aka kawo Bitrus da Yohanna a gabansu suka kuma fara yin musu tambayoyi cewa, “Da wane iko ko da wane suna kuka yi wannan?”
8 Alors Pierre, rempli de l'Esprit saint, leur dit: «Magistrats du peuple, et Anciens d'Israël,
Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki ya ce musu, “Masu mulki da dattawan mutane!
9 puisqu'on nous interroge aujourd'hui à l'occasion d'un bienfait accordé à un infirme, et qu'on nous demande par quoi cet homme a été guéri,
In ana tuhumarmu ne yau saboda alherin da aka yi wa gurgun nan da kuma yadda aka warkar da shi,
10 sachez bien, vous tous, et que tout le peuple d'Israël le sache aussi, que c'est par le nom de Jésus-Christ de Nazareth, que vous avez crucifié, mais que Dieu a ressuscité des morts: c'est par lui que cet homme se présente devant vous, guéri.
to, sai ku san wannan, ku da dukan mutanen Isra’ila cewa da sunan Yesu Kiristi Banazare, wanda kuka gicciye amma wanda Allah ya tasar daga matattu ne, wannan mutum yake tsaye a gabanku lafiyayye.
11 Jésus est «la pierre que vous, constructeurs, vous avez mise au rebut, mais qui est devenue la pierre angulaire; »
Shi ne, “‘dutsen da ku magina kuka ƙi, wanda kuwa ya zama dutsen kusurwar gini.’
12 et il n’y a point de salut en aucun autre, car il n'y a sous le ciel, parmi les hommes, aucun autre nom qui ait été donné, par lequel nous devions être sauvés.»
Ba a samun ceto ta wurin wani dabam, gama babu wani suna a ƙarƙashin sama da aka ba wa mutane wanda ta wurinsa dole mu sami ceto.”
13 Les sénateurs furent étonnés de voir l'assurance de Pierre et de Jean, d'autant qu'ils s'aperçurent que c'étaient des hommes du peuple sans instruction. Ils les reconnurent pour avoir été avec Jésus,
Da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yohanna suka kuma gane cewa su marasa ilimi ne, talakawa kuma, sai suka yi mamaki suka kuma lura cewa waɗannan mutane sun kasance tare da Yesu.
14 et, comme ils voyaient là, avec eux, l'homme qui avait été guéri, ils n'avaient rien à répondre.
Amma da yake sun ga mutumin da aka warkar yana tsaye a wurin tare da su, sai suka rasa abin faɗi.
15 Après les avoir fait sortir du sanhédrin, ils discutèrent entre eux, disant:
Saboda haka suka umarta a fitar da su daga Majalisar, sa’an nan suka yi shawara da juna.
16 «Que ferons-nous à ces hommes? Qu'ils aient fait un miracle insigne, c'est ce que tous les habitants de Jérusalem peuvent voir, et nous ne pouvons le nier;
Suka ce, “Me za mu yi da waɗannan mutane? Kowa da yake zama a Urushalima ya san sun yi abin banmamaki, kuma ba za mu iya yin mūsu wannan ba.
17 mais afin que cela ne se divulgue pas davantage, défendons-leur avec menaces de parler désormais à qui que ce soit en ce nom-là.»
Amma don a hana wannan abu daga ƙara bazuwa cikin mutane, dole mu kwaɓe mutanen nan kada su ƙara yi wa kowa magana cikin wannan suna.”
18 Et les ayant rappelés, ils leur interdirent absolument de parler et d'enseigner au nom de Jésus.
Sai suka sāke kiransu ciki suka kuma umarce su kada su kuskura su yi magana ko su ƙara koyarwa a cikin sunan Yesu.
19 Mais Pierre et Jean leur répondirent: «Jugez, s'il est juste devant Dieu, de vous écouter, plutôt que Dieu.
Amma Bitrus da Yohanna suka amsa, “Ku shari’anta da kanku ko daidai ne a gaban Allah mu yi muku biyayya maimakon Allah.
20 Pour nous, nous ne pouvons pas ne pas dire ce que nous avons vu et entendu.»
Gama ba za mu iya daina yin magana game da abin da muka gani muka kuma ji ba.”
21 Ils les renvoyèrent avec de nouvelles menaces, ne sachant comment les punir, à cause du peuple, parce que tout le monde glorifiait Dieu de ce qui était arrivé.
Bayan ƙarin barazana sai suka bar su su tafi. Ba su iya yanke shawara yadda za a hore su ba, domin dukan mutane suna yabon Allah saboda abin da ya faru.
22 En effet, l'homme qui avait été miraculeusement guéri, avait plus de quarante ans.
Gama mutumin da ya sami warkarwar banmamaki, shekarunsa sun fi arba’in.
23 Dès qu'on les eut relâchés, ils se rendirent auprès des leurs, et rapportèrent tout ce que les souverains sacrificateurs et les anciens leur avaient dit.
Da aka sake su, Bitrus da Yohanna suka koma wajen mutanensu suka ba da labarin duk abin da manyan firistoci da dattawa suka faɗa musu.
24 Après les avoir entendus, les frères élevèrent tous ensemble la voix vers Dieu, et dirent: «Souverain Maître, tu es le Dieu qui a fait le ciel, la terre, la mer et tout ce qu'ils renferment,
Sa’ad da suka ji wannan, sai suka ɗaga muryoyinsu gaba ɗaya cikin addu’a ga Allah, suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai ka halicci sama da ƙasa da kuma teku, da kome da yake cikinsu.
25 c'est toi qui as dit par la bouche de David ton serviteur: Pourquoi les nations ont-elles frémi de colère, et les peuples ont-ils formé de vains projets?
Ka yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki ta bakin bawanka, kakanmu Dawuda cewa, “‘Don me ƙasashe suke fushi, mutane kuma suke ƙulla shawara a banza?
26 Les rois de la terre se sont insurgés, et les magistrats se sont ligués contre le Seigneur et contre son Oint.»
Sarakunan duniya sun ja dāgā, masu mulki kuma sun taru gaba ɗaya, suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.’
27 En effet, Hérode et Ponce-Pilate se sont véritablement ligués, dans cette ville-ci, avec les nations et avec les peuples d'Israël contre ton serviteur Jésus, ton Oint,
Tabbatacce Hiridus da Buntus Bilatus suka haɗu tare da Al’ummai da kuma mutanen Isra’ila a wannan birni ce don su ƙulla gāba da bawanka mai tsarki Yesu, wanda ka shafe.
28 pour faire tout ce que ta main et ton conseil avaient arrêté;
Sun aikata abin da ikonka da kuma nufinka ya riga ya shirya tuntuni zai faru.
29 eh bien! maintenant vois leurs menaces, et donne à tes serviteurs d'annoncer ta parole avec pleine assurance,
Yanzu, Ubangiji, ka dubi barazanansu ka kuma sa bayinka su furta maganarka da iyakar ƙarfin hali.
30 en étendant ta main, pour qu'il s'opère des guérisons, et qu'il se fasse des miracles et des prodiges, par le nom de ton saint serviteur Jésus.
Ka miƙa hannunka don ka warkar ka kuma yi ayyukan banmamaki da alamu masu banmamaki ta wurin sunan bawanka mai tsarki Yesu.”
31 A peine eurent-ils prié, que le lieu où ils étaient réunis trembla: ils furent tous remplis du Saint-Esprit, et ils annoncèrent la parole de Dieu avec assurance.
Bayan suka yi addu’a, sai inda suka taru ya jijjigu. Dukansu kuwa suka cika da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta shaidar maganar Allah babu tsoro.
32 La multitude des croyants n'était qu'un coeur et qu'une âme. Personne ne disait que ce qu'il possédait était à lui en propre, mais tout était commun entre eux.
Dukan masu bi kuwa zuciyarsu ɗaya ne, nufinsu kuwa ɗaya. Babu wani da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, amma sun raba kome da suke da shi.
33 Les apôtres rendaient témoignage avec beaucoup de force de la résurrection du Seigneur Jésus, et une grande grâce était répandue sur eux tous;
Da iko mai ƙarfi manzanni suka ci gaba da shaidar tashin matattu na Ubangiji Yesu, alheri mai yawa kuwa yana bisansu duka.
34 car nul parmi eux n'était dans le besoin. Tous ceux qui se trouvaient possesseurs de terres ou de maisons, les vendaient, en apportaient le prix,
Babu mabukata a cikinsu. Lokaci-lokaci waɗanda suke da gonaki ko gidaje sukan sayar da su, su kawo kuɗi daga abin da suka sayar,
35 et le déposaient aux pieds des apôtres. Et l'on donnait à chacun selon le besoin qu'il en avait.
su ajiye a sawun manzannin, a kuma raba wa kowa gwargwadon bukatarsa.
36 Joses, surnommé par les apôtres Barnabas, c’est-à-dire, fils d'exhortation, lévite originaire de Chypre, possédait un champ;
Yusuf, wani Balawe daga Saifurus, wanda manzanni suke kira Barnabas (wanda yake nufin Ɗan Ƙarfafawa)
37 il le vendit, en apporta l'argent, et le déposa aux pieds des apôtres.
ya sayar da wata gonar da ya mallaki ya kuma kawo kuɗin ya ajiye a sawun manzanni.