< 1 Jean 5 >

1 Quiconque croit que Jésus est le Christ, est né de Dieu; et quiconque aime celui qui a engendré, aime aussi celui qui a été engendré.
Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
2 C'est à ceci que nous reconnaissons que nous aimons les enfants de Dieu: si nous aimons Dieu et si nous pratiquons ses commandements,
Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
3 car c'est aimer Dieu que de garder ses commandements. Et ses commandements ne sont pas pénibles,
Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
4 parce que tout ce qui est né de Dieu remporte la victoire sur le monde; et la puissance par laquelle le monde est vaincu, c'est notre foi.
domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
5 Qui est celui qui est vainqueur du monde, sinon celui qui croit que Jésus est le Fils de Dieu?
Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
6 Ce Jésus est bien celui qui est venu en passant par l'eau et par le sang, non par l'eau seulement, mais par l'eau et par le sang, Jésus le Christ; et l'Esprit est celui qui l'atteste, parce que l'Esprit est la vérité:
Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
7 il y en a, en effet, trois qui rendent témoignage,
Akwai shaidu uku, wato,
8 l'Esprit, l'eau et le sang, et ces trois sont unanimes dans leur témoignage.
Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
9 Si nous recevons le témoignage des hommes, le témoignage de Dieu est d'un plus grand poids; et c'est bien le témoignage de Dieu, puisqu'il a rendu témoignage à son Fils.
Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
10 Celui qui croit au Fils de Dieu, possède au dedans de lui ce témoignage: celui qui ne croit pas Dieu, le fait menteur, puisqu'il n'ajoute pas foi au témoignage que Dieu a rendu à son Fils.
Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
11 Et voici ce témoignage, c'est que Dieu nous a donné la vie éternelle, et que cette vie est dans son Fils. (aiōnios g166)
Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. (aiōnios g166)
12 Celui qui a le Fils a la vie; celui qui n'a pas le Fils de Dieu, n'a pas la vie.
Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
13 Je vous ai écrit ces choses, afin que vous sachiez que vous avez la vie éternelle, vous qui croyez au nom du Fils de Dieu. (aiōnios g166)
Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami. (aiōnios g166)
14 Et nous avons cette pleine confiance en Dieu, que, si nous demandons quelque chose selon sa volonté, il nous écoute;
Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
15 et dès que nous savons qu'il nous écoute, quoi que nous lui demandions, nous savons que nous possédons les choses que nous lui avons demandées.
In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
16 Si quelqu'un voit son frère commettre un péché qui n'entraîne pas la mort, il priera, et il lui donnera la vie, à celui, dis-je, qui ne commet pas un péché qui entraîne la mort. Il y a tel péché qui entraîne la mort; je ne dis pas qu'il prie pour ce péché-là.
Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
17 Toute injustice est un péché, et il y a tel péché qui n'entraîne pas la mort.
Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
18 Nous savons que quiconque est né de Dieu, ne pèche point: celui qui est né de Dieu, se garde lui-même, et le malin ne le touche point.
Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
19 Nous savons que nous sommes issus de Dieu, et que le monde entier est plongé dans le mal;
Mun san cewa mu’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
20 mais nous savons que le Fils de Dieu est venu, et qu'il nous a donné l'intelligence, afin que nous connaissions le vrai Dieu; et nous sommes en ce vrai Dieu, étant en son Fils, Jésus-Christ: il est bien le vrai Dieu et la vie éternelle. (aiōnios g166)
Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada. (aiōnios g166)
21 Chers enfants, gardez-vous des idoles.
’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.

< 1 Jean 5 >