< Sophonie 2 >

1 Examinez-vous, examinez-vous avec soin ô nation qui n'êtes pas aimable!
Ku tattaru, ku tattaru, Ya ku al’umma marar kunya,
2 Avant que le décret enfante, et que le jour passe comme de la balle; avant que l'ardeur de la colère de l'Eternel vienne sur vous, avant que le jour de la colère de l'Eternel vienne sur vous.
kafin ƙayyadadden lokacin nan yă zo ranan nan kuma ta share ku kamar ƙaiƙayi kuma kafin fushi mai tsanani na Ubangiji yă auko muku, kafin ranar fushin Ubangiji ta auko muku.
3 Vous, tous les débonnaires du pays, qui faites ce qu'il ordonne, cherchez l'Eternel, cherchez la justice, cherchez la débonnaireté; peut-être serez-vous mis en sûreté au jour de la colère de l'Eternel.
Ku nemi Ubangiji, dukanku ƙasashe masu tawali’u, ku da kuke yin abin da ya umarta. Ku nemi adalci da tawali’u; mai yiwuwa ku sami mafaka a ranar fushin Ubangiji.
4 Mais Gaza sera abandonnée, et Askélon sera en désolation; on chassera [les habitants] d'Asdod en plein Midi, et Hékron sera arrachée.
Za a yashe Gaza a kuma bar Ashkelon kango. Da tsakar rana Ashdod za tă zama babu kowa a kuma tumɓuke Ekron.
5 Malheur aux habitants de la contrée maritime, à la nation des Kéréthiens, la parole de l'Eternel est contre vous; Canaan, [qui es] le pays des Philistins, je te détruirai, tellement que personne n'y habitera.
Taku ta ƙare ku da kuke zama a bakin teku, Ya ku mutanen Keretawa; maganar Ubangiji tana gāba da ke, Ya ke Kan’ana, ƙasar Filistiyawa. “Zan hallaka ki kuma babu abin da zai rage.”
6 Et la contrée maritime ne sera que cabanes, que loges de bergers, et parcs de brebis.
Ƙasar da take a bakin teku, inda Keretawa suke zaune, za tă zama wurin da makiyaya da ta garken tumaki.
7 Et cette contrée sera pour le reste de la maison de Juda; ils paîtront dans ces lieux-là, et le soir ils feront leur gîte dans les maisons d'Askélon; car l'Eternel leur Dieu les visitera, et il ramènera leurs captifs.
Za tă zama mallakar raguwar gidan Yahuda; a can za su sami wurin kiwo. Da yamma za su kwanta a gidajen Ashkelon. Ubangiji Allahnsu zai lura da su; zai maido musu da martabarsu.
8 J'ai ouï les insultes de Moab, et les invectives des enfants de Hammon, dont ils ont diffamé mon peuple, et l'ont bravé sur leur frontière.
“Na ji irin zagin da Mowab take yi, da kuma ba’ar Ammonawa, waɗanda suka zagi mutanena suna kuma yi barazana a kan ƙasarsu.
9 C'est pourquoi, je suis vivant, dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël, que Moab sera comme Sodome, et les enfants de Mammon comme Gomorrhe, un lieu couvert d'orties, et une carrière de sel et de désolation à jamais; les restes de mon peuple les pilleront, et les restes de [ma] nation les posséderont.
Saboda haka, muddin ina raye,” in ji Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, “tabbatacce Mowab za tă zama kamar Sodom, Ammonawa kuma kamar Gomorra, ƙasa mai ciyayi da rammukan gishiri, ƙasa marar amfani har abada. Raguwar mutanena za su washe su; waɗanda suka rage na al’ummata za su gāda ƙasarsu.”
10 Ceci leur arrivera en échange de leur orgueil, parce qu'ils ont usé d'insultes et de vanteries, contre le peuple de l'Eternel des armées.
Wannan ne zai zama sakamakon girmankansu, saboda zagi da kuma ba’ar da suka yi wa mutanen Ubangiji Maɗaukaki.
11 L'Eternel sera terrible contre eux; car il amaigrira tous les dieux du pays; et on se prosternera devant lui, chacun de son lieu, même toutes les Iles des nations.
Ubangiji zai zama abin tsoro a gare su sa’ad da ya hallaka allolin ƙasar. Al’ummai a kowane bakin teku za su yi masa sujada, kowa a ƙasarsa.
12 Vous aussi [habitants] de Cus, vous serez blessés à mort par mon épée.
“Ku ma, ya Kushawa, za a kashe ku da takobina.”
13 Il étendra aussi sa main sur l'Aquilon, et il détruira l'Assyrie, et mettra Ninive en désolation, en un lieu aride comme un désert.
Zai kuma miƙa hannunsa gāba da arewa yă kuma hallaka Assuriya, zai mai da Ninebe kango gaba ɗaya ta kuma zama busasshiya kamar hamada.
14 Et les troupeaux feront leur gîte au milieu d'elle, et toutes les bêtes des nations, même le cormoran, et le butor logeront dans ses porteaux, la voix des oiseaux retentira à la fenêtre, la désolation sera au seuil, parce qu'il en aura abbatu des cèdres.
Garkuna za su kwanta a can, da kowace irin halitta, Mujiyar hamada da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta. Kukansu za tă ratsa tagogi, ɓuraguzai za su tare ƙofofin shiga, za a kware ginshiƙan al’ul.
15 C'est là cette ville remplie de joie, qui se tenait assurée, et qui disait en son cœur; c'est moi, et il n'y en a point d'autre que moi. Comment a-t-elle été réduite en désert, pour être le gîte des bêtes? Quiconque passera près d elle se moquera, et branlera sa main.
Birnin da yake harka ke nan da take zaune lafiya. Ta ce wa kanta, “Ni ce, kuma babu kamata.” Dubi irin kangon da ta zama mana, mazaunin namun jeji! Duk wanda ya wuce ta sai ya yi mata tsaki yana kaɗa kai.

< Sophonie 2 >