< Psaumes 96 >
1 Chantez à l'Eternel un nouveau cantique; vous toute la terre chantez à l'Eternel.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 Chantez à l'Eternel, bénissez son Nom, prêchez de jour en jour sa délivrance.
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Racontez sa gloire parmi les nations, [et] ses merveilles parmi tous les peuples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 Car l'Eternel [est] grand, et digne d'être loué; il [est] redoutable par-dessus tous les dieux;
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 Car tous les dieux des peuples [ne sont que des] idoles; mais l'Eternel a fait les cieux.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 La majesté et la magnificence [marchent] devant lui; la force et l'excellence sont dans son sanctuaire.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Familles des peuples rendez à l'Eternel, rendez à l'Eternel la gloire et la force.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Rendez à l'Eternel la gloire due à son Nom; apportez l'oblation, et entrez dans ses parvis.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Prosternez-vous devant l'Eternel avec une sainte magnificence; vous tous les habitants de la terre tremblez tout étonnés, à cause de la présence de sa face.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Dites parmi les nations: l'Eternel règne; même la terre habitable est affermie, [et] elle ne sera point ébranlée; il jugera les peuples en équité.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Que les cieux se réjouissent, et que la terre s'égaye! Que la mer et ce qui est contenu en elle bruie!
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 Que les champs s'égayent, avec tout ce qui est en eux. Alors tous les arbres de la forêt chanteront de joie,
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 Au-devant de l'Eternel, parce qu'il vient, parce qu'il vient pour juger la terre; il jugera en justice le monde habitable, et les peuples selon sa fidélité.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.