< Psaumes 89 >

1 Maskil d'Ethan Ezrahite. Je chanterai les bontés de l'Eternel à toujours; je manifesterai de ma bouche ta fidélité d'âge en âge.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Car j'ai dit: ta bonté continue à toujours, [comme] les cieux, tu as établi en eux ta fidélité [quand tu as dit]:
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 J'ai traité alliance avec mon élu, j'ai fait serment à David mon serviteur, [en disant]:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 J'établirai ta race à toujours, et j'affermirai ton trône d'âge en âge; (Sélah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Et les cieux célèbrent tes merveilles, ô Eternel! ta fidélité aussi [est] célébrée dans l'assemblée des Saints.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Car qui est-ce au-dessus des nues qui soit égal à l'Eternel? Qui est semblable à l'Eternel entre les fils des forts?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Le [Dieu] Fort se rend extrêmement terrible dans le Conseil secret des Saints, il est plus redouté que tous ceux qui sont à l'entour de lui.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Ô Eternel Dieu des armées, qui est semblable à toi, puissant Eternel? aussi ta fidélité est à l'entour de toi.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tu as puissance sur l'élévation des flots de la mer; quand ses vagues s'élèvent, tu les fais rabaisser.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tu as abattu Rahab comme un homme blessé à mort; tu as dissipé tes ennemis par le bras de ta force.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 A toi sont les cieux, à toi aussi est la terre; tu as fondé la terre habitable, et tout ce qui est en elle.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Tu as créé l'Aquilon et le Midi; Tabor et Hermon se réjouissent en ton Nom.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Tu as un bras puissant, ta main est forte, et ta droite est haut élevée.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 La justice et l'équité sont la base de ton trône; la gratuité et la vérité marchent devant ta face.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Ô que bienheureux est le peuple qui sait ce que c'est que du cri de réjouissance! Ils marcheront, ô Eternel! à la clarté de ta face.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Ils s'égayeront tout le jour en ton Nom, et ils se glorifieront de ta justice.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Parce que tu es la gloire de leur force; et notre pouvoir est distingué par ta faveur.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Car notre bouclier est l'Eternel, et notre Roi est le Saint d'Israël.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Tu as autrefois parlé en vision touchant ton bien-aimé, et tu as dit: J'ai ordonné mon secours en faveur d'un homme vaillant; j'ai élevé l'élu d'entre le peuple.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 J'ai trouvé David mon serviteur, je l'ai oint de ma sainte huile;
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Ma main sera ferme avec lui, et mon bras le renforcera.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 L'ennemi ne le rançonnera point, et l'inique ne l'affligera point;
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 Mais je froisserai devant lui ses adversaires, et je détruirai ceux qui le haïssent.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Ma fidélité et ma bonté seront avec lui; et sa gloire sera élevée en mon Nom.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Et je mettrai sa main sur la mer, et sa droite sur les fleuves.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Il m'invoquera, [disant: ] Tu es mon Père; mon [Dieu] Fort, et le Rocher de ma délivrance.
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Aussi je l'établirai l'aîné [et] le souverain sur les Rois de la terre.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Je lui garderai ma bonté à toujours, et mon alliance lui sera assurée.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Je rendrai éternelle sa postérité, et je ferai que son trône sera comme les jours des cieux.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Mais si ses enfants abandonnent ma Loi, et ne marchent point selon mes ordonnances;
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 S'ils violent mes statuts, et qu'ils ne gardent point mes commandements;
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Je visiterai de verge leur transgression, et de plaie leur iniquité.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Mais je ne retirerai point de lui ma bonté, et je ne lui fausserai point ma foi.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Je ne violerai point mon alliance, et je ne changerai point ce qui est sorti de mes lèvres.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 J'ai une fois juré par ma sainteté; (si je mens jamais à David; )
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Que sa race sera à toujours, et que son trône sera comme le soleil, en ma présence:
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Qu'il sera affermi à toujours comme la lune; et il y en aura dans les cieux un témoin certain; (Sélah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Néanmoins tu l'as rejeté, et l'as dédaigné; tu t'es mis en grande colère contre ton Oint.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Tu as rejeté l'alliance faite avec ton serviteur; tu as souillé sa couronne, [en la jetant] par terre.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Tu as rompu toutes ses cloisons; tu as mis en ruine ses forteresses.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Tous ceux qui passaient par le chemin l'ont pillé; il a été mis en opprobre à ses voisins.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Tu as élevé la droite de ses adversaires, tu as réjoui tous ses ennemis.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Tu as aussi émoussé la pointe de son épée, et tu ne l'as point redressé en la bataille.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Tu as fait cesser sa splendeur, et tu as jeté par terre son trône.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Tu as abrégé les jours de sa jeunesse, [et] l'as couvert de honte; (Sélah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Jusques à quand, ô Eternel? te cacheras-tu à jamais? ta fureur s'embrasera-t-elle comme un feu?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Souviens-toi de combien petite durée je suis; pourquoi aurais-tu créé en vain tous les fils des hommes?
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Qui est l'homme qui vivra, et ne verra point la mort, et qui garantira son âme de la main du sépulcre? (Sélah) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Seigneur, où sont tes bontés précédentes lesquelles tu as jurées à David sur ta fidélité?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Seigneur! souviens-toi de l'opprobre de tes serviteurs, [et comment] je porte dans mon sein [l'opprobre qui nous a été fait] par tous les grands peuples,
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 [L'opprobre] dont tes ennemis ont diffamé, ô Eternel! dont ils ont diffamé les traces de ton Oint.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Béni soit à toujours l'Eternel; Amen! Oui, Amen!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Psaumes 89 >