< Psaumes 88 >
1 Maskil d'Héman Ezrahite, [qui est] un Cantique de Psaume, [donné] au maître chantre d'entre les enfants de Coré, [pour le chanter] sur Mahalath-lehannoth. Eternel! Dieu de ma délivrance, je crie jour et nuit devant toi.
Waƙa ce, Zabura ta’ya’yan Kora maza. Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat leyannotmaskil na Heman dangin Ezra. Ya Ubangiji, Allah wanda ya cece ni, dare da rana ina kuka a gabanka.
2 Que ma prière vienne en ta présence; ouvre ton oreille à mon cri.
Bari addu’ata ta zo a gabanka; ka kasa kunne ga kukata.
3 Car mon âme a tout son saoul de maux, et ma vie est venue jusqu'au sépulcre. (Sheol )
Gama raina yana cike da wahala rayuwata tana gab da kabari. (Sheol )
4 On m'a mis au rang de ceux qui descendent en la fosse; je suis devenu comme un homme qui n'a plus de vigueur;
An lissafta ni cikin waɗanda suka gangara zuwa cikin rami; ni kamar mutumin da ba shi da ƙarfi ne.
5 Placé parmi les morts, comme les blessés à mort couchés au sépulcre, desquels il ne te souvient plus, et qui sont retranchés par ta main.
An ware ni tare da matattu, kamar waɗanda aka kashe da suke kwance a kabari, waɗanda ba ka ƙara tunawa, waɗanda aka yanke daga taimakonka.
6 Tu m'as mis en une fosse des plus basses, dans des lieux ténébreux, dans des lieux profonds.
Ka sa ni a ramin da yake can ƙasa cikin zurfafa mafi duhu.
7 Ta fureur s'est jetée sur moi, et tu m'as accablé de tous tes flots; (Sélah)
Hasalarka tana da nauyi a kaina; ka turmushe ni da dukan raƙumanka. (Sela)
8 Tu as éloigné de moi ceux de qui j'étais connu, tu m'as mis en une extrême abomination devant eux; je suis enfermé tellement, que je ne puis sortir.
Ka ɗauke abokaina na kurkusa daga gare ni ka sa na zama abin ƙyama a gare su. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta
9 Mon œil languit d'affliction; Eternel! je crie à toi tout le jour, j'étends mes mains vers toi.
idanuna ba sa gani sosai saboda baƙin ciki. Ina kira gare ka, ya Ubangiji, kowace rana; na tā da hannuwana zuwa gare ka.
10 Feras-tu un miracle envers les morts? ou les trépassés se relèveront-ils pour te célébrer? (Sélah)
Kakan nuna wa matattu ayyukanka na banmamaki ne? Waɗanda suka mutu sukan tashi su yabe ka ne? (Sela)
11 Racontera-t-on ta miséricorde dans le sépulcre? [et] ta fidélité dans le tombeau?
Ana furta ƙaunar a cikin kabari ne, ana zancen amincinka a cikin Hallaka ne?
12 Connaîtra-t-on tes merveilles dans les ténèbres; et ta justice au pays d'oubli?
An san ayyukanka masu banmamaki a wurin duhu ne, ko ayyukan adalcinka a lahira?
13 Mais moi, ô Eternel! je crie à toi, ma prière te prévient dès le matin.
Amma ina kuka gare ka neman taimako, ya Ubangiji; da safe addu’ata kan zo gabanka.
14 Eternel! pourquoi rejettes-tu mon âme, pourquoi caches-tu ta face de moi?
Don me, ya Ubangiji, ka ƙi ni ka kuma ɓoye fuskarka daga gare ni?
15 Je suis affligé et comme rendant l'esprit dès ma jeunesse; j'ai été exposé à tes terreurs, et je ne sais où j'en suis.
Tun ina ƙarami na sha wahala na kuma yi kusa in mutu; na sha wahalar razanarka kuma na kuma fid da zuciya.
16 Les ardeurs de ta [colère] sont passées sur moi, et tes frayeurs m'ont retranché.
Hasalarka ta sha kaina; razanarka ta hallaka ni.
17 Ils m'ont tout le jour environné comme des eaux, ils m'ont entouré tous ensemble.
Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa; sun mamaye ni ɗungum.
18 Tu as éloigné de moi mon ami, même mon intime ami, et ceux de qui je suis connu me sont des ténèbres.
Ka ɗauke abokaina da ƙaunatattuna daga gare ni; duhu ne abokina na kurkusa.