< Psaumes 78 >

1 Maskil d'Asaph. Mon peuple, écoute ma Loi, prêtez vos oreilles aux paroles de ma bouche.
Maskil na Asaf. Ya mutanena, ku ji koyarwata; ku saurari kalmomin bakina.
2 J'ouvrirai ma bouche en similitudes: je manifesterai les choses notables du temps d'autrefois.
Zan buɗe bakina da misalai, zan faɗi ɓoyayyun abubuwa, abubuwan dā,
3 Lesquelles nous avons ouïes et connues, et que nos pères nous on racontées.
abin da muka ji muka kuma sani, abubuwan da kakanninmu suka faɗa mana.
4 Nous ne les cèlerons point à leurs enfants, [et] ils raconteront à la génération à venir les louanges de l'Eternel, et sa force, et ses merveilles qu'il a faites.
Ba za mu ɓoye su wa’ya’yanmu ba; za mu faɗa wa tsara mai zuwa ayyukan da suka zama yabo na Ubangiji, ikonsa, da abubuwan banmamakin da ya aikata.
5 Car il a établi le témoignage en Jacob, et il a mis la Loi en Israël; et il donna charge à nos pères de les faire entendre à leurs enfants.
Ya kafa ƙa’idodi wa Yaƙub ya kuma kafa doka a cikin Isra’ila, wadda ya umarce kakanni-kakanninmu su koya wa’ya’yansu,
6 Afin que la génération à venir, les enfants, [dis-je], qui naîtraient, les connut, [et] qu'ils se missent en devoir de les raconter à leurs enfants;
don tsara na biye su san su, har da’ya’yan da ba a riga an haifa ba, su kuma su faɗa wa’ya’yansu.
7 Et afin qu'ils missent leur confiance en Dieu, et qu'ils n'oubliassent point les exploits du [Dieu] Fort, et qu'ils gardassent ses commandements.
Ta haka za su dogara ga Allah ba kuwa za su manta da ayyukansa ba amma za su kiyaye umarnansa.
8 Et qu'ils ne fussent point, comme leurs pères, une génération revêche et rebelle, une génération qui n'a point soumis son cœur, et l'esprit de laquelle n'a point été fidèle au [Dieu] Fort.
Ba za su zama kamar kakanni kakanninsu ba, masu taurinkai da kuma tsara masu tayarwa, waɗanda zukatansu ba su yi biyayya ga Allah ba, waɗanda zukatansu ba su yi aminci ga Allah ba.
9 Les enfants d'Ephraïm armés entre les archers, ont tourné le dos le jour de la bataille.
Mutanen Efraim, ko da yake suna da bakkuna, suka juya da baya a ranar yaƙi;
10 Ils n'ont point gardé l'alliance de Dieu, et ont refusé de marcher selon sa Loi.
ba su kiyaye alkawarin Allah ba suka kuma ƙi su yi rayuwa ta wurin dokarsa.
11 Et ils ont mis en oubli ses exploits et ses merveilles qu'il leur avait fait voir.
Suka manta da abin da ya aikata, abubuwan banmamakin da ya nuna musu.
12 Il a fait des miracles en la présence de leurs pères au pays d'Egypte, au territoire de Tsohan.
Ya yi mu’ujizai a idanun kakanninsu a ƙasar Masar, a yankin Zowan.
13 Il a fendu la mer, et les a fait passer au travers, et il a fait arrêter les eaux comme un monceau [de pierre].
Ya raba teku ya kuma bi da su ciki; ya sa ruwa ya tsaya daram kamar bango.
14 Et il les a conduits de jour par la nuée, et toute la nuit par une lumière de feu.
Ya bishe su da girgije da rana da kuma haske daga wuta dukan dare.
15 Il a fendu les rochers au désert, et leur a donné abondamment à boire, comme [s'il eût puisé] des abîmes.
Ya tsage duwatsu a cikin hamada ya kuma ba su ruwaye a yalwace kamar tekuna;
16 Il a fait, dis-je, sortir des ruisseaux de la roche, et en a fait découler des eaux comme des rivières.
ya fid da rafuffuka daga dutsen da ya tsaga ya sa ruwa ya gudu kamar koguna.
17 Toutefois ils continuèrent à pécher contre lui, irritant le Souverain au désert.
Amma suka ci gaba da yin masa zunubi, suna tayarwa a cikin hamada a kan Mafi Ɗaukaka.
18 Et ils tentèrent le [Dieu] Fort dans leurs cœurs, en demandant de la viande qui flattât leur appétit.
Da gangan suka gwada Allah ta wurin neman abincin da suke kwaɗayi.
19 Ils parlèrent contre Dieu, disant: le [Dieu] Fort nous pourrait-il dresser une table en ce désert?
Suka yi magana a kan Allah, suna cewa, “Allah zai iya shimfiɗa tebur a cikin hamada?
20 Voilà, [dirent-ils], il a frappé le rocher, et les eaux en sont découlées, et il en est sorti des torrents abondamment, mais pourrait-il aussi nous donner du pain? apprêterait-il bien de la viande à son peuple?
Sa’ad da ya bugi dutse, ruwa ya ɓulɓulo, rafuffuka suka yi gudu a yalwace. Amma zai iya ba mu abinci? Zai iya tanada wa mutanensa nama?”
21 C'est pourquoi l'Eternel les ayant ouïs, se mit en grande colère, et le feu s'embrasa contre Jacob, et sa colère s'excita contre Israël.
Sa’ad da Ubangiji ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; wutarsa ta ɓarke a kan Yaƙub, hasalarsa kuwa ta tashi a kan Isra’ila,
22 Parce qu'ils n'avaient point cru en Dieu, et ne s'étaient point confiés en sa délivrance.
gama ba su gaskata ga Allah ba ko su dogara ga cetonsa.
23 Bien qu'il eût donné commandement aux nuées d'en haut, et qu'il eût ouvert les portes des cieux;
Duk da haka ya ba da umarni ga sarari a bisa ya kuma buɗe ƙofofin sammai;
24 Et qu'il eût fait pleuvoir la manne sur eux afin qu'ils en mangeassent, et qu'il leur eût donné le froment des cieux;
ya sauko da Manna wa mutanensa don su ci, ya ba su hatsin sama.
25 Tellement que chacun mangeait du pain des puissants. Il leur envoya donc de la viande pour s'en rassasier.
Mutane suka ci burodin mala’iku; ya aika musu dukan abincin da za su iya ci.
26 Il excita dans les cieux le vent d'Orient, et il amena par sa force le vent du midi.
Ya saki iskar gabas daga sammai ya kuma saki iskar yamma ta wurin ikonsa.
27 Et il fit pleuvoir sur eux de la chair comme de la poussière, et des oiseaux volants, en une quantité pareille au sable de la mer.
Ya sauko da nama a kansu kamar ƙura, tsuntsaye masu firiya kamar yashi a bakin teku.
28 Et il la fit tomber au milieu de leur camp, [et] autour de leurs pavillons.
Ya sa suka sauka a cikin sansaninsu, ko’ina kewaye da tentunansu.
29 Et ils en mangèrent, et en furent pleinement rassasiés, car il avait accompli leur souhait.
Suka ci har suka sami fiye da abin da ya ishe su, gama ya ba su abin da suka yi kwaɗayi.
30 [Mais] ils n'en avaient pas encore perdu l'envie, et leur viande était encore dans leur bouche.
Amma kafin su juyo daga abincin da suka yi kwaɗayi, kai tun ma yana a bakunansu,
31 Quand la colère de Dieu s'excita contre eux, et qu'il mit à mort les gras d'entre eux, et abattit les gens d'élite d'Israël.
fushin Allah ya ƙuna a kansu; ya karkashe waɗanda suka fi ƙiba a cikinsu, yana yankan matasan Isra’ila.
32 Nonobstant cela, ils péchèrent encore, et n'ajoutèrent point de foi à ses merveilles.
Duk da haka, suka ci gaba da yin zunubi; duk da abubuwan banmamakinsa, ba su gaskata ba.
33 C'est pourquoi il consuma soudainement leurs jours, et leurs années promptement.
Saboda haka ya sa kwanakinsu suka ƙare a banza shekarunsu kuma cikin masifa.
34 Quand il les mettait à mort, alors ils le recherchaient, ils se repentaient, et ils cherchaient le [Dieu] Fort dès le matin.
A duk sa’ad da Allah ya kashe su, sai su neme shi; sukan juyo a natse gare shi.
35 Et ils se souvenaient que Dieu était leur rocher, et que le [Dieu] Fort et Souverain était celui qui les délivrait.
Sun tuna cewa Allah ne Dutsensu, cewa Allah Mafi Ɗaukaka ne Mai fansarsu.
36 Mais ils faisaient beau semblant de leur bouche, et ils lui mentaient de leur langue;
Amma sai su yi ta yin masa zaƙin baki, suna masa ƙarya da harsunansu;
37 Car leur cœur n'était point droit envers lui, et ils ne furent point fidèles en son alliance.
zukatansu ba sa biyayya gare shi, ba su da aminci ga alkawarinsa.
38 Toutefois, comme il est pitoyable, il pardonna leur iniquité, tellement qu'il ne les détruisit point, mais il apaisa souvent sa colère, et n'émut point toute sa fureur.
Duk da haka ya kasance mai jinƙai; ya gafarta laifofinsu bai kuwa hallaka su ba. Sau da sau ya janye fushinsa bai kuwa sa fushinsa yă ƙuna ba.
39 Et il se souvint qu'ils n'étaient que chair, qu'un vent qui passe, et qui ne revient point.
Ya tuna cewa su naman jiki ne kawai, iska mai wucewa da ba ta dawowa.
40 Combien de fois l'ont-ils irrité au désert, et combien de fois l'ont-ils ennuyé dans ce lieu inhabitable?
Sau da yawa sun tayar masa a cikin hamada suka kuma ɓata masa rai a jeji!
41 Car coup sur coup ils tentaient le [Dieu] Fort; et bornaient le Saint d'Israël.
Sau da sau suka riƙa gwada Allah; suka tsokane Mai Tsarki na Isra’ila.
42 Ils ne se sont point souvenus de sa main, ni du jour qu'il les avait délivrés de la main de celui qui les affligeait.
Ba su tuna da ikonsa, a ranar da ya fanshe su daga mai danniya,
43 [Ils ne se sont point souvenus] de celui qui avait fait ses signes en Egypte, et ses miracles au territoire de Tsohan:
ranar da ya nuna mu’ujizansa a Masar abubuwan banmamakinsa a yankin Zowan ba.
44 Et qui avait changé en sang leurs rivières et leurs ruisseaux, afin qu'ils n'en pussent point boire.
Ya mai da kogunansu suka zama jini; ba su iya sha daga rafuffuka ba.
45 Et qui avait envoyé contre eux une mêlée de bêtes, qui les mangèrent; et des grenouilles, qui les détruisirent.
Ya aika da tarin ƙudajen da suka cinye su, da kwaɗin da suka wahalshe su.
46 Et qui avait donné leurs fruits aux vermisseaux, et leur travail aux sauterelles.
Ya ba da hatsinsu ga fāra, amfanin gonakinsu ga ɗango.
47 Qui avait détruit leurs vignes par la grêle, et leurs sycomores par les orages.
Ya lalace inabinsu da ƙanƙara itatuwan al’ul nasu kuma da jaura.
48 Et qui avait livré leur bétail à la grêle, et leurs troupeaux aux foudres étincelantes.
Ya miƙa shanunsu ga ƙanƙara, tumakinsu ga aradun tsawa.
49 Qui avait envoyé sur eux l'ardeur de sa colère, grande colère, indignation et détresse, [qui sont] un envoi de messagers de maux.
Ya saki musu fushinsa mai zafi, hasalarsa, zafin rai da kuma ɓacin ransa, ƙungiyar mala’iku masu hallakarwa.
50 Qui avait dressé le chemin à sa colère, et n'avait point retiré leur âme de la mort; et qui avait livré leur bétail à la mortalité.
Ya shirya hanya wa fushinsa; bai tsare ransu daga mutuwa ba amma ya miƙa su ga annoba.
51 Et qui avait frappé tout premier-né en Egypte, les prémices de la vigueur dans les tentes de Cam.
Ya bugi kowane ɗan fari na Masar, mafari ƙarfin mazantakansu a tentunan Ham.
52 Qui avait fait partir son peuple comme des brebis; et qui l'avait mené par le désert comme un troupeau.
Amma ya fitar da mutanensa kamar garke; ya bi da su kamar tumaki ta cikin hamada.
53 Et qui les avait conduits sûrement, et sans qu ils eussent aucune frayeur, là où la mer couvrit leurs ennemis.
Ya bi da su lafiya ƙalau, don kada su ji tsoro; amma teku ya cinye abokan gābansu.
54 Et qui les avait introduits en la contrée de sa Sainteté, [savoir] en cette montagne que sa droite a conquise.
Ta haka ya kawo su iyakar ƙasa mai tsarki, zuwa ƙasar tudun da hannunsa na dama ya kame.
55 Et qui avait chassé de devant eux les nations qu'il leur a fait tomber en lot d'héritage, et avait fait habiter les Tribus d'Israël dans les tentes de ces nations.
Ya kori al’ummai a gabansu ya rarraba ƙasashensu gare su a matsayin gādo; ya zaunar da kabilan Isra’ila a gidajensu.
56 Mais ils ont tenté et irrité le Dieu Souverain, et n'ont point gardé ses témoignages.
Amma suka gwada Allah suka tayar wa Mafi Ɗaukaka; ba su kiyaye ƙa’idodinsa ba.
57 Et ils se sont retirés en arrière, et se sont portés infidèlement, ainsi que leurs pères; ils se sont renversés comme un arc qui trompe.
Kamar kakanninsu suka zama marasa biyayya da marasa aminci, marar tabbas kamar tanƙwararren baka.
58 Et ils l'ont provoqué à la colère par leurs hauts lieux, et l'ont ému à la jalousie par leurs images taillées.
Suka ba shi haushi da masujadansu na kan tudu; suka tayar da kishinsa da gumakansu.
59 Dieu l'a ouï, et s'est mis en grande colère, et il a fort méprisé Israël.
Sa’ad da Allah ya ji su, ya yi fushi ƙwarai; ya ƙi Isra’ila gaba ɗaya.
60 Et il a abandonné le pavillon de Silo, le Tabernacle où il habitait entre les hommes.
Ya yashe tabanakul na Shilo, tentin da ya kafa a cikin mutane.
61 Et il a livré en captivité sa force et son ornement entre les mains de l'ennemi.
Ya aika da akwatin alkawarin ƙarfinsa zuwa bauta, darajarsa zuwa cikin hannuwan abokin gāba.
62 Et il a livré son peuple à l'épée et s'est mis en grande colère contre son héritage.
Ya ba da mutanensa ga takobi; ya yi fushi ƙwarai da gādonsa.
63 Le feu a consumé leurs gens d'élite, et leurs vierges n'ont point été louées.
Wuta ta cinye matasansu maza,’yan matansu kuma ba su da waƙoƙin aure;
64 Leurs Sacrificateurs sont tombés par l'épée, et leurs veuves ne les ont point pleuré.
aka karkashe firistocinsu, gwaurayensu kuwa ba su iya makoki ba.
65 Puis le Seigneur s'est réveillé comme un homme qui se serait endormi, et comme un puissant homme qui s'écrie ayant encore le vin dans la tête.
Sa’an nan Ubangiji ya farka sai ka ce daga barcinsa, kamar yadda mutum kan farka daga buguwar ruwan inabi.
66 Et il a frappé ses adversaires par derrière, et les a mis en opprobre perpétuel.
Ya kori abokan gābansa; ya sa suka sha madawwamiyar kunya.
67 Mais il a dédaigné le Tabernacle de Joseph, et n'a point choisi la Tribu d'Ephraïm.
Sa’an nan ya ƙi tentunan Yusuf, bai zaɓi kabilar Efraim ba;
68 Mais il a choisi la Tribu de Juda, la montagne de Sion, laquelle il aime;
amma ya zaɓi kabilar Yahuda, Dutsen Sihiyona, wanda ya ƙaunaci.
69 Et il a bâti son Sanctuaire comme [des bâtiments] haut élevés, et l'a établi comme la terre qu'il a fondée pour toujours.
Ya gina wurinsa mai tsarki kamar bisa, kamar duniyar da ya kafa har abada.
70 Et il a choisi David, son serviteur, et l'a pris des parcs des brebis;
Ya zaɓi Dawuda bawansa ya kuma ɗauke shi daga ɗakin tumaki;
71 [Il l'a pris, dis-je, ] d'après les brebis qui allaitent, et l'a amené pour paître Jacob son peuple, et Israël son héritage.
daga kiwon tumaki ya kawo shi don yă kuma zama makiyayin mutanensa Yaƙub, na Isra’ila gādonsa.
72 Aussi les a-t-il fait repus selon l'intégrité de son cœur, et conduits par la sage direction de ses mains.
Dawuda kuwa ya zama makiyayinsu da mutuncin zuciya; da hannuwa masu gwaninta ya bi da su.

< Psaumes 78 >