< Psaumes 66 >
1 Cantique de Psaume, [donné] au maître chantre. Toute la terre, jetez des cris de réjouissance à Dieu.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Psalmodiez la gloire de son Nom, rendez sa louange glorieuse.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Dites à Dieu: ô que tu es terrible en tes exploits! Tes ennemis te mentiront à cause de la grandeur de ta force.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 Toute la terre se prosternera devant toi, et te psalmodiera; elle psalmodiera ton Nom; (Sélah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Venez, et voyez les œuvres de Dieu: il est terrible en exploits sur les fils des hommes.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 Il a fait de la mer une terre sèche; on a passé le fleuve à pied sec; [et] là nous nous sommes réjouis en lui.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 Il domine par sa puissance éternellement; ses yeux prennent garde sur les nations; les revêches ne se pourront point élever; (Sélah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Peuples, bénissez notre Dieu, et faites retentir le son de sa louange.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 C'est lui qui a remis notre âme en vie, et qui n'a point permis que nos pieds bronchassent.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 Car, ô Dieu! tu nous avais sondés, tu nous avais affinés comme on affine l'argent.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Tu nous avais amenés aux filets, tu avais mis une étreinte en nos reins.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Tu avais fait monter les hommes sur notre tête, et nous étions entrés dans le feu et dans l'eau; mais tu nous as fait entrer en un lieu fertile.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 J'entrerai dans ta maison avec des holocaustes; [et] je te rendrai mes vœux.
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Lesquels mes lèvres ont proférés, et que ma bouche a prononcés, lorsque j'étais en détresse.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 Je t'offrirai des holocaustes de bêtes mœlleuses, avec la graisse des moutons, laquelle on fait fumer; je te sacrifierai des taureaux et des boucs; (Sélah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Vous tous qui craignez Dieu, venez, écoutez, et je raconterai ce qu'il a fait à mon âme.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 Je l'ai invoqué de ma bouche, et il a été exalté par ma langue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 Si j'eusse médité quelque outrage dans mon cœur, le Seigneur ne m'eût point écouté.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 Mais certainement Dieu m'a écouté, [et] il a été attentif à la voix de ma supplication.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Béni soit Dieu qui n'a point rejeté ma supplication, et qui n'a point éloigné de moi sa gratuité.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!