< Psaumes 64 >

1 Psaume de David, [donné] au maître chantre. Ô Dieu! écoute ma voix quand je m'écrie; garde ma vie de la frayeur de l'ennemi.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
2 Tiens-moi caché loin du secret conseil des malins, [et] de l'assemblée tumultueuse des ouvriers d'iniquité;
Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
3 Qui ont aiguisé leur langue comme une épée; et qui ont tiré pour leur flèche une parole amère.
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4 Afin de tirer contre celui qui est juste jusque dans le lieu où il se croyait en sûreté; ils tirent promptement contre lui; et ils n'ont point de crainte.
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5 Ils s'assurent sur de mauvaises affaires, [et] tiennent des discours pour cacher des filets; [et] ils disent: Qui les verra?
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6 Ils cherchent curieusement des méchancetés; ils ont sondé tout ce qui se peut sonder, même ce qui peut être au-dedans de l'homme, et au cœur le plus profond.
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
7 Mais Dieu a subitement tiré son trait contr’eux, et ils en ont été blessés.
Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
8 Et ils ont fait tomber sur eux-mêmes leur propre langue; ils iront çà et là; chacun les verra.
Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
9 Et tous les hommes craindront, et ils raconteront l'œuvre de Dieu, et considéreront ce qu'il aura fait.
Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
10 Le juste se réjouira en l'Eternel, et se retirera vers lui; et tous ceux qui sont droits de cœur s'en glorifieront.
Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!

< Psaumes 64 >