< Psaumes 60 >
1 Mictam de David, [propre] pour enseigner, [et donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Susan-heduth. Touchant la guerre qu'il eut contre la Syrie de Mésopotamie, et contre la Syrie de Tsoba; et touchant ce que Joab retournant défit douze mille Iduméens dans la vallée du sel. Ô Dieu! tu nous as rejetés, tu nous as dispersés, tu t'es courroucé; retourne-toi vers nous.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin Alkawari.” Wani miktam ta Dawuda. Don koyarwa. Sa’ad da ya yaƙi Aram-Naharayim da Aram-Zoba, da kuma sa’ad da Yowab ya dawo ya bugi mutanen Edom dubu goma sha biyu a Kwarin Gishiri. Ka ki mu, ya Allah, ka kuma fashe kāriyarmu; ka yi fushi da mu, yanzu ka mai da mu!
2 Tu as ébranlé la terre, et l'as mise en pièces; répare ses fractures, car elle est affaissée.
Ka girgiza ƙasar ka kuma tsaga ta; ka daure karayarta, gama tana rawa.
3 Tu as fait voir à ton peuple des choses dures, tu nous as abreuvés de vin d'étourdissement.
Ka nuna wa mutanenka lokutan wahala; ka ba mu ruwan inabin da ya sa muka bugu.
4 [Mais depuis] tu as donné une bannière à ceux qui te craignent, afin de l'élever en haut pour l'amour de ta vérité; (Sélah)
Amma ga waɗanda suke tsoronka, ka ɗaga tuta don a buɗe gāba da baka. (Sela)
5 Afin que ceux que tu aimes soient délivrés. Sauve-moi par ta droite, et exauce-moi.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
6 Dieu a parlé dans son Sanctuaire; je me réjouirai; je partagerai Sichem, et je mesurerai la vallée de Succoth.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Da nasara zan rarraba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
7 Galaad sera à moi, Manassé aussi sera à moi, et Ephraïm sera la force de mon chef, Juda sera mon législateur.
Gileyad nawa ne, Manasse kuma nawa ne; Efraim shi ne hular kwanona, Yahuda kuma sandar mulkina.
8 Moab sera le bassin où je me laverai; je jetterai mon soulier à Edom; Ô Palestine, triomphe à cause de moi.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirarin nasara.”
9 Qui sera-ce qui me conduira en la ville munie? Qui sera-ce qui me conduira jusques en Edom?
Wa zai kawo ni birnin katanga? Wa zai bishe ni zuwa Edom?
10 Ne sera-ce pas toi, ô Dieu! qui nous avais rejetés, et qui ne sortais plus, ô Dieu! avec nos armées.
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
11 Donne-nous du secours [pour sortir] de détresse; car la délivrance [qu'on attend] de l'homme est vanité.
Ka ba mu gudummawa a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
12 Nous ferons des actions de valeur [avec le secours de] Dieu, et il foulera nos ennemis.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattake abokan gābanmu.