< Psaumes 55 >

1 Maskil de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Néguinoth. Ô Dieu! prête l'oreille à ma requête, et ne te cache point arrière de ma supplication.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Wani maskil ta Dawuda. Ka ji addu’ata, ya Allah, kada ka ƙyale roƙona;
2 Ecoute-moi, et m'exauce, je verse des larmes dans ma méditation et je suis agité.
ka ji ni ka kuma amsa mini. Tunanina yana damuna na kuma gaji tilis
3 A cause du bruit que fait l'ennemi, [et] à cause de l'oppression du méchant; car ils font tomber sur moi tout outrage, et ils me haïssent jusques à la fureur.
hankalina ya tashi saboda yawan surutan masu ƙina, saboda danniyar mugaye. Gama sukan jawo mini wahala, suna jin haushina suna ƙina.
4 Mon cœur est au-dedans de moi comme en travail d'enfant, et des frayeurs mortelles sont tombées sur moi.
Zuciyata tana wahala a cikina; tsorace-tsoracen mutuwa sun sha kaina.
5 La crainte et le tremblement se sont jetés sur moi, et l'épouvantement m'a couvert.
Tsoro da rawan jiki sun kama ni; razana ta sha kaina.
6 Et j'ai dit: Ô qui me donnerait des ailes de pigeon? je m'envolerais, et je me poserais en quelque endroit.
Na ce, “Kash, da a ce ina da fikafikan kurciya mana! Ai, da na yi firiya na tafi na huta,
7 Voilà, je m'enfuirais bien loin, et je me tiendrais au désert; (Sélah)
da na tafi can da nisa na zauna a hamada; (Sela)
8 Je me hâterais de me garantir de ce vent excité par la tempête.
da na hanzarta na tafi wurin mafakata, nesa da muguwar iska da hadiri.”
9 Seigneur, engloutis-les, divise leur langue; car j'ai vu la violence et les querelles en la ville.
Ka rikitar da mugaye, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, gama na ga rikici da faɗa a cikin birni.
10 Elles l'environnent jour et nuit sur ses murailles; l'outrage et le tourment sont au milieu d'elle.
Dare da rana suna yawo a kan katanga; mugun hali da zargi suna a cikinta.
11 Les calamités sont au milieu d'elle, et la tromperie et la fraude ne partent point de ses places.
Rundunar hallaka suna aiki a cikin birni; barazana da ƙarairayi ba sa taɓa barin titunanta.
12 Car ce n'est pas mon ennemi qui m'a diffamé, autrement je l'eusse souffert; [ce] n'est point celui qui m'a en haine qui s'est élevé contre moi, autrement je me fusse caché de lui.
Da a ce abokin gāba ne ke zagina, da na jure da shi; da a ce maƙiyi yana tā da kansa a kaina, da na ɓoye daga gare shi.
13 Mais c'est toi, ô homme! qui étais estimé autant que moi, mon gouverneur, et mon familier;
Amma kai ne, mutum kamar ni, abokina, abokina na kurkusa,
14 Qui prenions plaisir à communiquer [nos] secrets ensemble, [et] qui allions de compagnie en la maison de Dieu.
wanda na taɓa jin daɗin zumunci da shi sosai yayinda muke tafiya tare a taron jama’a a gidan Allah.
15 Que la mort, comme un exacteur, se jette sur eux! qu'ils descendent tous vifs en la fosse! Car il n'y a que des maux parmi eux dans leur assemblée. (Sheol h7585)
Bari mutuwa ta ɗauki abokan gābana ba labari; bari su gangara da rai zuwa cikin kabari, gama mugunta tana samun masauƙi a cikinsu. (Sheol h7585)
16 [Mais] moi je crierai à Dieu, et l'Eternel me délivrera.
Amma na kira ga Allah, Ubangiji kuwa ya cece ni.
17 Le soir, et le matin, et à midi je parlerai et je m'émouvrai, et il entendra ma voix.
Safe, rana da yamma ina kuka da nishi, yakan kuwa ji muryata.
18 Il délivrera mon âme en paix de la guerre qu'on me fait; car j'ai à faire contre beaucoup de gens.
Yakan fisshe ni lafiya daga yaƙin da ake yi da ni, ko da yake da yawa suna gāba da ni.
19 Le [Dieu] Fort l'entendra, et les accablera; car il préside de toute ancienneté; (Sélah) Parce qu'il n'y a point de changement en eux, et qu'ils ne craignent point Dieu.
Allah, yana mulki har abada, zai ji su yă kuma azabtar da su, (Sela) mutanen da ba sa taɓa canja hanyoyinsu kuma ba sa tsoron Allah.
20 [Chacun d'eux] a jeté ses mains sur ceux qui vivaient paisiblement avec lui, [et] a violé son accord.
Abokina ya kai wa abokansa hari; ya tā da alkawarinsa.
21 Les paroles de sa bouche sont plus douces que le beurre, mais la guerre est dans son cœur; ses paroles sont plus douces que l'huile, néanmoins elles sont tout autant d'épées nues.
Maganarsa tana da laushi kamar man zaitun, duk da haka yaƙi yana a cikin zuciyarsa; kalmominsa sun fi mai sulɓi, duk da haka takuba ne zārarru.
22 Rejette ta charge sur l'Eternel, et il te soulagera: il ne permettra jamais que le juste tombe.
Ku kawo damuwoyinku ga Ubangiji zai kuwa riƙe ku; ba zai taɓa barin mai adalci yă fāɗi ba.
23 Mais toi, ô Dieu! tu les précipiteras au puits de la perdition: les hommes sanguinaires et trompeurs ne parviendront point à la moitié de leurs jours: mais je m'assurerai en toi.
Amma kai, ya Allah, za ka kawar da mugaye zuwa cikin ramin lalacewa; masu kisa da mutane masu ruɗu ba za su kai rabin kwanakin rayuwarsu ba. Amma ni dai, na dogara gare ka.

< Psaumes 55 >