< Psaumes 53 >
1 Maskil de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Mahalath. L'insensé dit en son cœur: Il n'y a point de Dieu. Ils se sont corrompus, ils ont rendu abominable leur perversité; il n'y a personne qui fasse bien.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Bisa ga mahalat. Wani maskil na Dawuda. Wawa ne kawai yakan ce a zuciyarsa, “Ba Allah.” Sun lalace, kuma hanyoyinsu ba su da kyau; babu wani mai aikata abu mai kyau.
2 Dieu a regardé des Cieux sur les fils des hommes, pour voir s'il y en a quelqu'un qui soit intelligent, [et] qui cherche Dieu.
Allah yana duba daga sama a kan’ya’yan mutane yă ga ko akwai wani wanda ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 Ils se sont tous retirés en arrière, [et] se sont tous rendus odieux: il n'y a personne qui fasse bien, non pas même un seul.
Kowa ya kauce, gaba ɗaya sun lalace; babu guda da yake aikata abu mai kyau, babu ko ɗaya.
4 Les ouvriers d'iniquité n'ont-ils point de connaissance, mangeant mon peuple, [comme] s'ils mangeaient du pain? Ils n'invoquent point Dieu.
Masu aikata mugunta ba sa taɓa koyo? Suna cin mutanena kamar yadda ake cin burodi, ba sa kuma kira ga Allah.
5 Ils seront extrêmement effrayés là où ils n'avaient point eu de peur; car Dieu a dispersé les os de celui qui se campe contre toi. Tu les as rendus confus, parce que Dieu les a rendus contemptibles.
Ga shi fa, sun firgita don tsoro, ko da yake babu dalilin tsoro, gama Allah zai watsar da ƙasusuwan masu ƙinsa, za su sha kunya, gama Allah ya ƙi su.
6 Ô qui donnera de Sion les délivrances d'Israël? Quand Dieu aura ramené son peuple captif, Jacob s'égayera, Israël se réjouira.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Allah ya sāke arzuta mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!