< Psaumes 44 >
1 Maskil des enfants de Coré, [donné] au maître chantre. Ô Dieu nous avons ouï de nos oreilles, [et] nos pères nous ont raconté les exploits que tu as faits en leurs jours, aux jours d'autrefois.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’ya’yan Kora maza. Maskil ne. Mun ji da kunnuwanmu, ya Allah; kakanninmu sun faɗa mana abin da ka aikata a kwanakinsu, tun dā can.
2 Tu as de ta main chassé les nations, et tu as affermi nos [pères]; tu as affligé les peuples, et tu as fait prospérer nos pères.
Da hannunka ka kori al’ummai ka kuma dasa kakanninmu; ka ragargaza mutanen ka kuma sa kakanninmu suka haɓaka.
3 Car ce n'est point par leur épée qu'ils ont conquis le pays, et ce n'a point été leur bras, qui les a délivrés; mais ta droite, et ton bras, et la lumière de ta face; parce que tu les affectionnais.
Ba da takobinsu ba ne suka ci ƙasar, ba kuwa ƙarfin hannunsu ne ya ba su nasara ba; hannun damanka ne, ƙarfin hannunka, da kuma hasken fuskarka, gama ka ƙaunace su.
4 Ô Dieu! c'est toi qui es mon Roi, ordonne les délivrances de Jacob.
Kai ne Sarkina da kuma Allahna, wanda ya ba da nasarori wa Yaƙub.
5 Avec toi nous battrons nos adversaires, par ton Nom nous foulerons ceux qui s'élèvent contre nous.
Ta wurinka mun tura abokan gābanmu baya; ta wurin sunanka muka tattake maƙiyanmu.
6 Car je ne me confie point en mon arc, et ce ne sera pas mon épée qui me délivrera;
Ba na dogara ga bakana, takobina ba ya kawo nasara;
7 Mais tu nous délivreras de nos adversaires, et tu rendras confus ceux qui nous haïssent.
amma kana ba mu nasara a kan abokan gābanmu, ka sa abokan gābanmu suka sha kunya.
8 Nous nous glorifierons en Dieu tout le jour, et nous célébrerons à toujours ton Nom. (Sélah)
A cikin Allah muke fariyarmu dukan yini, kuma za mu yabi sunanka har abada. (Sela)
9 Mais tu nous as rejetés, et rendus confus, et tu ne sors plus avec nos armées.
Amma yanzu ka ƙi mu ka kuma ƙasƙantar da mu; ba ka ƙara fita tare da mayaƙanmu.
10 Tu nous as fait retourner en arrière de devant l'adversaire, et nos ennemis se sont enrichis de ce qu'ils ont pillé sur nous.
Ka sa muka gudu a gaban abokin gāba, kuma abokan gābanmu suka washe mu.
11 Tu nous as livrés comme des brebis destinées à être mangées, et tu nous as dispersés entre les nations.
Ka ba da mu a cinye kamar tumaki ka kuma watsar da mu a cikin al’ummai.
12 Tu as vendu ton peuple pour rien, et tu n'as point fait hausser leur prix.
Ka sayar da mutanenka a kuɗin da bai taka ƙara ya karye ba babu wata riba daga sayar da su da ka yi.
13 Tu nous as mis en opprobre chez nos voisins, en dérision, et en raillerie auprès de ceux qui habitent autour de nous.
Ka mai da mu abin dariya ga maƙwabtanmu, abin dariya da reni ga waɗanda suke kewaye da mu.
14 Tu nous as mis en dicton parmi les nations, [et] en hochement de tête parmi les peuples.
Ka sa muka zama abin ba’a a cikin al’ummai; mutanen suna kaɗa mana kai.
15 Ma confusion est tout le jour devant moi, et la honte de ma face m'a tout couvert.
Dukan yini ina cikin wulaƙanci, fuskata kuma ta rufu da kunya
16 A cause des discours de celui qui [nous] fait des reproches, et qui nous injurie, [et] à cause de l'ennemi et du vindicatif.
saboda ba’ar waɗanda suke zagi suke kuma ƙina, saboda abokan gābana, waɗanda suka sha alwashi sai sun yi ramuwa.
17 Tout cela nous est arrivé, et cependant nous ne t'avons point oublié, et nous n'avons point faussé ton alliance.
Dukan wannan ya faru da mu, ko da yake ba mu manta da kai ba ko mu kasance masu ƙarya ga alkawarinka.
18 Notre cœur n'a point reculé en arrière, ni nos pas ne se sont point détournés de tes sentiers;
Zukatanmu ba su juya baya; ƙafafunmu ba su kauce daga hanyarka ba.
19 Quoique tu nous aies froissés parmi des dragons, et couverts de l'ombre de la mort.
Amma ka ragargaza mu ka kuma maishe mu abin farautar karnukan jeji ka kuma rufe mu cikin duhu baƙi ƙirin.
20 Si nous eussions oublié le Nom de notre Dieu, et que nous eussions étendu nos mains vers un dieu étranger,
Da a ce mun manta da sunan Allahnmu ko mun miƙa hannuwanmu ga baƙin alloli,
21 Dieu ne s'en enquerrait-il point? vu que c'est lui qui connaît les secrets du cœur.
da Allah bai gane ba, da yake ya san asiran zuciya?
22 Mais nous sommes tous les jours mis à mort pour l'amour de toi, [et] nous sommes regardés comme des brebis de la boucherie.
Duk da haka saboda kai mun fuskanci mutuwa dukan yini; aka ɗauke mu kamar tumakin da za a yanka.
23 Lève-toi, pourquoi dors-tu, Seigneur? Réveille-toi, ne nous rejette point à jamais.
Ka farka, ya Ubangiji! Don me kake barci? Ta da kanka! Kada ka ƙi mu har abada.
24 Pourquoi caches-tu ta face, [et] pourquoi oublies-tu notre affliction et notre oppression?
Me ya sa ka ɓoye fuskarka ka manta da azabanmu da kuma danniyar da ake mana?
25 Car notre âme est penchée jusques en la poudre, et notre ventre est attaché contre terre.
An kai mu ƙasa zuwa ƙura; jikunanmu sun manne da ƙasa.
26 Lève-toi pour nous secourir, et nous délivre pour l'amour de ta gratuité.
Ka tashi ka taimake mu; ka cece mu saboda ƙaunarka marar ƙarewa.