< Psaumes 14 >

1 Psaume de David, [donné] au maître chantre. L'insensé a dit en son cœur: il n'y a point de Dieu. Ils se sont corrompus, ils se sont rendus abominables en leurs actions; il n'y a personne qui fasse le bien.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Wawaye sukan ce a ransu, “Ba Allah.” Sun lalace, ayyukansu kuwa mugaye ne; babu wani da yake yi abu mai kyau.
2 L'Eternel a regardé des cieux sur les fils des hommes, pour voir s'il y en a quelqu'un qui soit intelligent, [et] qui cherche Dieu.
Ubangiji ya duba daga sama a kan’yan adam don yă ga ko akwai wani da ya gane, wani wanda yake neman Allah.
3 Ils se sont tous égarés, ils se sont tous ensemble rendus odieux, il n'y a personne qui fasse le bien, non pas même un seul.
Duka sun kauce, duka gaba ɗaya sun zama lalatattu; babu ɗaya wanda yake yin abu mai kyau, ba ko ɗaya.
4 Tous ces ouvriers d'iniquité n'ont-ils point de connaissance? Ils mangent mon peuple [comme] s'ils mangeaient du pain, ils n'invoquent point l'Eternel.
Masu aikata mugunta za su taɓa koyo. Suna cin mutane yadda mutane ke cin gurasa kuma waɗanda ba sa kira bisa Ubangiji?
5 Là ils seront saisis d'une grande frayeur; car Dieu est avec la race juste.
Ga su, tsoro ya sha kansu, gama Allah yana cikin ƙungiyar adalai.
6 Vous faites honte à l'affligé de ce qu'il s'est proposé l'Eternel pour sa retraite.
Ku masu mugunta kuna sa ƙoƙarin matalauta yă zama banza, amma Ubangiji ne mafakansu.
7 Ô! qui donnera de Sion la délivrance d'Israël! Quand l'Eternel aura ramené son peuple captif, Jacob s'égaiera, Israël se réjouira.
Kash, da ceton Isra’ila zai fito daga Sihiyona mana! Sa’ad da Ubangiji zai maido da sa’ar mutanensa, bari Yaƙub yă yi farin ciki Isra’ila kuma yă yi murna!

< Psaumes 14 >