< Psaumes 135 >
1 Louez le Nom de l’Eternel; vous serviteurs de l'Eternel, louez-le.
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 Vous qui assistez en la maison de l'Eternel, aux parvis de la maison de notre Dieu,
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Louez l'Eternel, car l'Eternel est bon; psalmodiez à son Nom, car il est agréable.
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Car l'Eternel s'est choisi Jacob, et Israël pour son plus précieux joyau.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Certainement je sais que l'Eternel est grand, et que notre Seigneur [est] au-dessus de tous les dieux.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 L'Eternel fait tout ce qu'il lui plaît, dans les cieux et sur la terre, dans la mer, et dans tous les abîmes.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 C'est lui qui fait monter les vapeurs du bout de la terre; il fait les éclairs pour la pluie; il tire le vent hors de ses trésors.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 C'est lui qui a frappé les premiers-nés d'Egypte, tant des hommes que des bêtes;
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 Qui a envoyé des prodiges et des miracles au milieu de toi, ô Egypte! contre Pharaon, et contre tous ses serviteurs;
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 Qui a frappé plusieurs nations, et tué les puissants Rois;
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 [Savoir], Sihon le roi des Amorrhéens, et Hog le roi de Hasan, et ceux de tous les Royaumes de Canaan;
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 Et qui a donné leur pays en héritage, en héritage, [dis-je], à Israël son peuple.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Eternel, ta renommée est perpétuelle; Eternel, la mémoire qu'on a de toi est d'âge en âge.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Car l'Eternel jugera son peuple, et se repentira à l'égard de ses serviteurs.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Les dieux des nations ne sont que de l'or et de l'argent, un ouvrage de mains d'homme.
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 Ils ont une bouche, et ne parlent point; ils ont des yeux, et ne voient point;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 Ils ont des oreilles, et n'entendent point; il n'y a point aussi de souffle dans leur bouche.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Que ceux qui les font, [et] tous ceux qui s'y confient, leur soient faits semblables.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Maison d'Israël, bénissez l'Eternel; maison d'Aaron, bénissez l'Eternel.
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Maison des Lévites, bénissez l'Eternel; vous qui craignez l'Eternel, bénissez l'Eternel.
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Béni soit de Sion l'Eternel qui habite dans Jérusalem. Louez l'Eternel.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.