< Psaumes 130 >

1 Cantique Mahaloth. Ô Éternel! je t'invoque des lieux profonds.
Waƙar haurawa. Daga cikin zurfafa na yi kuka gare ka, ya Ubangiji;
2 Seigneur, écoute ma voix! que tes oreilles soient attentives à la voix de mes supplications.
Ya Ubangiji, ka ji muryata. Bari kunnuwanka su saurara ga kukata ta neman jinƙai.
3 Ô Eternel! si tu prends garde aux iniquités, Seigneur, qui est-ce qui subsistera?
In kai, ya Ubangiji, za ka lissafta zunubai, Ya Ubangiji, wa zai tsaya?
4 Mais il y a pardon par-devers toi, afin que tu sois craint.
Amma tare da kai akwai gafartawa, saboda haka ake tsoronka.
5 J'ai attendu l'Eternel; mon âme l'a attendu, et j'ai eu mon attente en sa parole.
Zan jira Ubangiji, raina zai jira, kuma a cikin maganarsa na sa zuciyata.
6 Mon âme [attend] le Seigneur plus que les sentinelles [n'attendent] le matin, plus que les sentinelles [n'attendent] le matin.
Raina na jiran Ubangiji fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya, fiye da yadda mai tsaro yakan jira safiya.
7 Israël, attends-toi à l'Eternel: car l'Eternel est miséricordieux et il y a rédemption en abondance par devers lui.
Ya Isra’ila, sa zuciya ga Ubangiji, gama tare da Ubangiji akwai ƙauna marar ƙarewa kuma tare da shi akwai cikakkiyar fansa.
8 Et lui-même rachètera Israël de toutes ses iniquités.
Shi kansa zai fanshi Isra’ila daga dukan zunubansu.

< Psaumes 130 >