< Psaumes 122 >

1 Cantique de Mahaloth, de David. Je me suis réjoui à cause de ceux qui me disaient: nous irons à la maison de l'Eternel.
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Nos pieds se sont arrêté en tes portes, ô Jérusalem!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jérusalem, qui est bâtie comme une ville dont les habitants sont fort unis,
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 A laquelle montent les Tribus, les Tribus de l'Eternel, ce qui est un témoignage à Israël, pour célébrer le Nom de l’Eternel.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 Car c'est là qu'ont été posés les sièges pour juger, les sièges, [dis-je], de la maison de David.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Priez pour la paix de Jérusalem; que ceux qui t'aiment jouissent de la prospérité.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Que la paix soit à ton avant-mur, et la prospérité dans tes palais.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 Pour l'amour de mes frères et de mes amis, je prierai maintenant pour ta paix.
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 A cause de la maison de l'Eternel notre Dieu je procurerai ton bien.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Psaumes 122 >