< Psaumes 11 >
1 Psaume de David, [donné] au maître chantre. Je me suis retiré vers l'Eternel; comment [donc] dites-vous à mon âme: Fuis-t'en en votre montagne, oiseau?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don busa. Ta Dawuda. A wurin Ubangiji ne nake samun mafaka. Yaya za ku ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu.
2 En effet, les méchants bandent l'arc, ils ont ajusté leur flèche sur la corde, pour tirer en secret contre ceux qui sont droits de cœur.
Gama duba, mugaye sun tanƙware bakkunansu; sun kuma ɗana kibiyoyinsu don su harbi mutanen kirki a zuciya daga cikin duhu.
3 Puisque les fondements sont ruinés, que fera le juste?
Sa’ad da aka tumɓuke tushe, me adali zai iya yi?”
4 L'Eternel est au palais de sa Sainteté; l'Eternel a son Trône aux cieux; ses yeux contemplent, [et] ses paupières sondent les fils des hommes.
Ubangiji yana cikin haikalinsa mai tsarki; Ubangiji yana a kursiyinsa a sama. Yana kallon’ya’yan mutane; idanunsa suna bincike su.
5 L'Eternel sonde le juste et le méchant; et son âme hait celui qui aime la violence.
Ubangiji yana bincike adalai, amma ransa yana ƙi mugaye da masu son rikici.
6 Il fera pleuvoir sur les méchants des filets, du feu, et du souffre; et un vent de tempête sera la portion de leur breuvage.
A kan mugaye zai zuba garwashin wuta mai zafi da kuma kibiritu; iska mai zafi zai zama rabonsu.
7 Car l'Eternel juste aime la justice, ses yeux contemplent l'homme droit.
Gama Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar gaskiya masu adalci za su ga fuskarsa.