< Psaumes 108 >
1 Cantique de Psaume de David. Mon cœur est disposé, ô Dieu! ma gloire l'est aussi, je chanterai et je psalmodierai.
Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
2 Réveille-toi, ma musette et ma harpe, je me réveillerai à l'aube du jour.
Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
3 Eternel, je te célébrerai parmi les peuples, et je te psalmodierai parmi les nations.
Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
4 Car ta bonté est grande par-dessus les cieux, et ta vérité atteint jusqu’aux nues.
Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
5 Ô Dieu! élève-toi sur les cieux, et que ta gloire soit sur toute la terre.
A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
6 Afin que ceux que tu aimes soient délivrés; sauve-moi par ta droite, et exauce-moi.
Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
7 Dieu a parlé en son Sanctuaire; je me réjouirai; je partagerai Sichem, et mesurerai la vallée de Succoth.
Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
8 Galaad sera à moi, Manassé [sera] à moi, et Ephraïm sera ma principale force, Juda mon Législateur.
Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
9 Moab sera le bassin où je me laverai, je jetterai mon soulier sur Edom, je triompherai de la Palestine.
Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
10 Qui sera-ce qui me conduira en la ville munie? qui sera-ce qui me conduira jusques en Edom?
Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
11 Ne sera-ce pas toi, ô Dieu! qui nous avais rejetés, et qui ne sortais plus, ô Dieu! avec nos armées?
Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
12 Donne-nous secours pour sortir de la détresse; car la délivrance [qu'on attend] de l'homme est vaine.
Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
13 Nous ferons des actions de valeur en Dieu, et il foulera nos ennemis.
Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.