< Psaumes 105 >
1 Célébrez l'Eternel, invoquez son Nom, faites connaître parmi les peuples ses exploits.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Chantez-lui, psalmodiez-lui, parlez de toutes ses merveilles.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 Glorifiez-vous du Nom de sa sainteté, [et] que le cœur de ceux qui cherchent l'Eternel se réjouisse.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 Recherchez l'Eternel, et sa force; cherchez continuellement sa face.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Souvenez-vous de ses merveilles qu'il a faites, de ses miracles, et des jugements de sa bouche.
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 La postérité d'Abraham sont ses serviteurs; les enfants de Jacob sont ses élus;
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 Il est l'Eternel notre Dieu; ses jugements sont sur toute la terre.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 Il s'est souvenu à toujours de son alliance, de la parole qu'il a commandée en mille générations;
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Du traité qu'il a fait avec Abraham, et du serment qu'il a fait à Isaac,
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 Lequel il a ratifié pour être une ordonnance à Jacob, [et] à Israël [pour] être une alliance éternelle;
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 En disant: je te donnerai le pays de Canaan, pour le lot de ton héritage;
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Encore qu'ils fussent un petit nombre de gens, et qu'ils y séjournassent peu de temps comme étrangers.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 Car ils allaient de nation en nation, et d'un Royaume vers un autre peuple.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 Il ne souffrit pas qu'aucun les opprimât: et il a même châtié des Rois pour l'amour d'eux.
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 [Disant]: Ne touchez point à mes Oints, et ne faites point de mal à mes Prophètes.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 Il appela aussi la famine sur la terre, [et] rompit tout le bâton du pain.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 Il envoya un personnage devant eux; Joseph fut vendu pour esclave.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 On lui enserra les pieds en des ceps, sa personne fut mise aux fers.
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 Jusqu’au temps que sa parole fût venue, et que la parole de l'Eternel l'eût éprouvé.
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 Le Roi envoya, et on le relâcha; le dominateur des peuples [envoya], et on le délia.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 Il l'établit pour maître sur sa maison, et pour dominateur sur tout son domaine;
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 Pour soumettre les principaux à ses désirs, et pour instruire ses Anciens.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 Puis Israël entra en Egypte, et Jacob séjourna au pays de Cam.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 Et l'[Eternel] fit extrêmement multiplier son peuple, et le rendit plus puissant que ceux qui l'opprimaient.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 Il changea leur cœur, de sorte qu'ils eurent son peuple en haine, jusques à conspirer contre ses serviteurs.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 Il envoya Moïse son serviteur, [et] Aaron, qu'il avait élu.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 [Lesquels] accomplirent sur eux les prodiges, et les miracles qu'ils avaient eu charge de faire dans le pays de Cam.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 Il envoya les ténèbres, et fit obscurcir [l'air]; et ils ne furent point rebelles à ses ordres.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 Il convertit leurs eaux en sang, et fit mourir leurs poissons.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 Leur terre produisit en abondance des grenouilles, jusqu’au dedans des cabinets de leurs Rois.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 Il parla, et une mêlée de bêtes vint, et des poux sur tout leur pays.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 Il fit que leurs pluies furent de la grêle, [et] qu'il y eut sur leur terre un feu flamboyant.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 Il frappa leurs vignes, et leurs figuiers, et il brisa les arbres de leur pays.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 Il commanda, et les sauterelles vinrent, et des hurebecs sans nombre;
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 Qui broutèrent toute l'herbe en leur pays, et qui dévorèrent le fruit de leur terroir.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 Et il frappa tout premier-né dans leur pays, qui étaient les prémices de toute leur vigueur.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 Puis il les tira dehors avec de l'or et de l'argent, et il n'y eut aucun qui chancelât parmi ses Tribus.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 L'Egypte se réjouit à leur départ; car la peur qu'ils avaient d'eux, les avait saisis.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 Il étendit la nuée pour couverture, et le feu pour éclairer la nuit.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 [Le peuple] demanda, et il fit venir des cailles, et il les rassasia du pain des cieux.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 Il ouvrit le rocher, et les eaux en coulèrent; et coururent par les lieux secs, [comme] une rivière.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 Car il se souvint de la parole de sa sainteté, laquelle il avait donnée à Abraham son serviteur.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 Et il tira dehors son peuple avec allégresse, et ses élus avec chant de joie.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 Il leur donna les pays des nations, et ils possédèrent le fruit du travail des peuples.
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 Afin qu'ils gardassent ses statuts, et qu'ils observassent ses lois. Louez l'Eternel.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.